ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

by Sulaiman and Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
4 years ago
Kabarin Annabi SAW

An so idan akwai hali, mai ziyara ya yi kwana takwas a Madina yana gabatar da sallolin farillan nan guda biyar
tare da Annabi (SAW) a Masallacinsa. Ma’ana mutum yana sallah ga kuma Annabi (SAW) a Masallacin.

Idan kuma Hukumar Alhazai ba ta bari ba, shikenan. Ko na kwana daya mutum ya yi da Annabi (SAW) ya isa dukkan falala.

  • Ziyarar Kabarin Annabi (SAW) 1

Dole ne ko wane Musulmin Kwarai ya girmama Manzon Allah (SAW) ya daraja shi tare da bin sa.
A cikin Alkur’ani maigirma Allah (SWT) ya ce, &kuot;Mu muka aiko ka – ya Rasulallahi a matsayin – maishaida, maibishara, maigargadi (ga al’ummarka), – ku kuma al’ummarsa – ku yi imani da Allah, da Manzonsa, ku daraja shi, ku kai matukar girma wurin daraja shi.&kuot;
Malam Mubarridu ya ce ma’anar &kuot;wa tu’azziruhu&kuot; a cikin ayar ita ce &kuot;ku kai matuka cikin girmama Manzon Allah (SAW).

ADVERTISEMENT

Don haka Musulmi kar su yarda wani ya rude su ya yi musu dodorido idan an ga suna girmama Annabi (SAW) a ce musu ‘yan bid’ah sai su ji shakka su daina. Da irin wannan fahimtar ce aka je aka tada wa Annabi (SAW) bom a Masallacinsa.

Hatta Sahabban Annabi (SAW) sun fuskanci irin haka, babu abin da ba a fada musu ba, an ce musu wawaye saboda sun yi imani kuma duk abin da Manzon Allah (SAW) ya ce su yi ba sai sun tambaya ba, kawai yi suke.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Malamai sun bayyana cewa girmama Manzon Allah (SAW) bayan rasuwarsa, daidai yake da girmama shi kamar lokacin da yake da rai, babu banbanci. Kamar yadda ka san idan ka je gabansa yana raye za ka yi ladabi, haka ma yanzu idan ka je kabarinsa.

Yana daga girmama Manzon Allah (SAW) idan za ka ambaci sunansa, kar ka yi kamar na sauran mutane, ka sanya ladabi da natsuwa. Shi ya sa galibi masoyansa suka fi kiran mutanen da aka sanya musu sunansa (SAW) da lakabi. Maimakon Muhammadu, sai a rika fadar lakabin Nura, Hadi, Amin, Kamal, Nazir, Kamil da sauran su. Sannan da an ambaci sunan ka yi ma sa salati.

Haka nan yana daga girmama shi (SAW), idan mutum zai karanta Hadisinsa, ya yi shiga mai kyau tare da natsuwa da kankantar da kai. Haka nan ya girmama Sunnarsa.
Ma’anar Sunnah ita ce abin da Annabi (SAW) ya yi ko ya umurci a yi ko kuma aka yi a gabansa bai hana ba.
Amma ba kamar yadda wasu ke dauka ba musamman a kwanan nan, raina Allah da Manzonsa da wulakanta darajojin iyalan gidan Annabi (SAW) da sahabbansa a matsayin Sunnah.

Yana daga girmama Manzon Allah (SAW) da son sa, mutum ya rika shaukin jin tarihinsa da girmama iyalan gidansa da sahabbansa da malaman Musulunci magada Annabawa da duk wani abu da ya rataya da shi (SAW). Tun daga kan garin da ya zauna a ciki, da gidansa, da kayan da ya yi amfani da su har ma da ire-iren abincin da ya fi so da suturar sawa, duk a so su, a ga girmansu, ballantana kuma kabarinsa
Ya zo cikin Hadisi madaukaki cewa &kuot;Mumini ana binne shi ne a kasar da aka gina shi da ita.&kuot; Ma’ana duk inda aka binne mutum, da kasar wurin ne aka kwaba aka yi halittarsa da ita.
Kenan kasar Madina tana da matukar girma, don da ita ce aka gina Manzon Allah (SAW) da ita. Koda yake za a iya cewa ta yaya aka haife shi a Makka ba a Madina ba? To Abdullahi bin Abbas (RA) ya ruwaito Hadisin da cewa &kuot;lokacin da aka yi ruwan dufana ne Allah ya tafiyar da kasar halittarsa (SAW) zuwa Makka.&kuot;
Saboda haka kamar yadda Annabi (SAW) ya kasance mafificin Dan Adam, to kasar da aka yi halittarsa da ita ita ce mafificiyar kasa. Kuma shi ya sa Manzon Allah (SAW) ya ce &kuot;Ba domin yin Hijira – don Zatin Allah – ba (daga Makka zuwa Madina) da a Madina ma aka haife ni&kuot;. Tirmizi ya ruwaito Hadisin.
Domin fitar da abin a fili ma, Kakar-Kakar Manzon Allah (SAW) Salma’a wadda ta auri Hashimu ‘yar Madina ce daga kabilar Banin Najjar. Haka nan don Allah ya nuna wa mutane lamarin, sai Mahaifinsa Sayyidina Abdullahi (RA) ya zo ya rasu a Madina a lokacin da ya ziyarci dangin Kakarsa Salma’a. A da akwai gidan da ake zuwa ana ziyarar kabarin Kafin Ahlu Sa’ud su kama Madina su rufe wurin.
Ita ma Mahaifiyarsa Sayyida Amina (RA) ta ziyarci mijinta, Baban Annabi (SAW) tare da shi, da Ummu Aimana, a kan hanyarta ta komawa daga Madina ta rasu a Ab’wa. Daga Madina zuwa Ab’wa kilomita 150 ne. Amma tsakanin wurin da Makka kilomita 250.
Ibn Baddalu ya ce &kuot;Kamshin Madina ya ninka na ko ina&kuot;. Imamu Malik (RA) ya yi fatawa a yi wa wani mutum da ya ce kasar Madina lalatacciya ce bulala 30 kuma a kulle shi a kurkuku. Sai aka ce ma sa wannan mutumin babba ne fa? Sai ya ce &kuot;Ai ba bulala ya dace a yi ma sa ba, a daki wuyarsa kawai.&kuot; Ma’ana a kashe shi.
Akwai sabani a kan wadda ta fi daraja tsakanin Makka da aka haife shi (SAW) da Madina wadda ya yi Hijira kuma ya rasu a can. Ko wacce akwai Sahabbai da Malamai da suka goyi bayan fifikonta. Amma a wurin mu Malikawa, Madina ta fi daraja.
Sannan da Malikawan da sauran malaman Maz’habobin duk sun yi ittifakin cewa nan Shabbakin Manzon Allah (SAW) da ke kunshe da jikinsa ya fi ko wane wuri a kan kasa. An ciro wannan ne daga Tajuddinis subki. Shi kuma ya sake cirowa daga Ibn Akilul Hambali cewa &kuot;Wurin da aka binne Manzon Allah (SAW) ya fi har Al’arshi&kuot;.
Za mu dakata a nan sai Allah ya kai mu mako mai zuwa insha Allahu. Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadiy wa ala alihi hakka kadirihi wa mikdarihil aziym.

Kabarin Annabi SAW
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Kabarin Annabi SAW
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Kabarin Annabi SAW
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.