ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

by Sadiq
1 year ago
Mali

An kama tsohon Firaministan Mali, Choguel Kokalla Maïga, bisa tuhumar cin hanci, rashawa da ɓarnatar da kadarorin gwamnati. 

Wannan na zuwa ne bayan rahoton wani bincike da ya gano wasu kashe-kashe na kuɗin gwamnati ba bisa ƙa’ida ba a lokacin da Maïga yake riƙe da ofishin Firaminista da kuma jagorantar Universal Access Fund (AGEFAU).

  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
  • Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

Rahoton ya bayyana cewa an kashe kuɗaɗen ba tare da hujja ba, kamar kashe miliyan 15 na CFA a liyafar rana guda a garin Konobougou, alhali dokar kashe kuɗi ta iyakance irin wannan taro zuwa 75,000 CFA.

ADVERTISEMENT

Haka kuma an gano wasu kuɗaɗe da aka fitar don balaguro da ayyuka ba tare da hujja mai karfi ba.

Bayan fitar rahoton, an gayyaci Maïga tare da wasu tsoffin mataimakansa da suka haɗa da Issiaka Ahmadou Singaré, tsohon shugaban ma’aikata, daraktan kuɗi da gudanarwa na ofishin Firaminista, da wasu manyan jami’an AGEFAU domin yin bayani.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Lauyan Maïga, Cheick Oumar Konaré, ya bayyana cewa kamun bai dace ba saboda Maïga ba shi da niyyar guduwa ko lalata shaidu, yana kuma zargin cewa wannan wani mataki ne na siyasa saboda tsohon Firaministan ya daɗe yana sukar gwamnatin soja tun bayan tsawaita mulkinsu ba tare da gudanar da zaɓe ba.

Maïga, ya hau kujerar Firaminista a watan Yulin 2021 bayan gwamnatin sojoji ta yi juyin mulki, inda ya goyi bayan dakatar da shirye-shiryen zaɓe don bai wa gwamnatin soja ƙarin lokaci.

Sai dai daga baya ya fara sukar wasu matakan gwamnati, musamman bayan an dakatar da shi daga kujerarsa a watan Nuwamban 2024.

Tun bayan juyin mulkin 2020 da na 2021, Mali ta kasance ƙarƙashin mulkin soja, kuma ana zargin gwamnati da take haƙƙin ɗan adam da murƙushe ‘yan adawa.

A kwanakin baya ma an kama wasu sojoji bisa zargin kitsa juyin mulki.

Kamun Maïga ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar, inda wasu ke ganin matakin a matsayin wani yunƙuri na yaƙi da cin hanci, yayin da wasu kuma ke kallonsa a matsayin dabarar murjushe ‘yan adawa, musamman a wannan lokaci da ake buƙatar haɗin kai don dawo da tsarin dimokuraɗiyya a Mali.

MASU ALAKA

Mali
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Mali
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Mali
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe 'Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

September 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing

September 17, 2026
Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

September 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

September 17, 2026
Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

September 17, 2026
Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

September 17, 2026
 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

September 17, 2026
2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.