ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC

by Sulaiman
1 year ago
Uba sani

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC ya kaddamar da gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC gabanin zaben Shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli da ke tafe a jihar Kaduna a ranar 19 ga watan Oktoba.
Gwamna Sani ya mika tutoci ga ‘yan takarar shugabannin kananan hukumomi a karkashin jam’iyyar APC daga kananan hukumomi 23 da ke jihar.
  • A Shirye Nake Na Rantse Da Alkur’ani Ban Saci Kudin Kaduna Ba – El-Rufai
  • Murnar Ƴanci: Gwamna Fintiri Ya Yafe Wa Fursunoni Biyu
Da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci gangamin yakin neman zaben da za a yi a watan Oktoba, Gwamnan ya bayyana irin gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a muhimman sassa a fadin jihar, musamman ta fuskar farfado da yankunan karkara da samar da ababen more rayuwa.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa, tun bayan hawansa mulki, gwamnatinsa ta ba da fifiko wajen raya karkara, inda ta kaddamar da gina tituna 62 a fadin kananan hukumomi 23.
A bangaren Ilimi, gwamnatin ta gina makarantun sakandire 60. Bugu da kari, an rage adadin yaran da ba sa zuwa makaranta da 300,000 ta hanyar sabin tsarin ilimi da sabuwar gwamnatin ta kirkiro.
Uba sani
Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannin kiwon lafiya, inda ya ce, an kammala inganta manyan cibiyoyin kula da lafiya 9, yayin da ake kan gina wasu sabbi 4, sannan kuma, an samar wa cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko 290 kayayyakin aiki.
Gwamnan ya jaddada cewa, kula da lafiya ba alfarma ba ce, hakki ne ga al’ummar jihar Kaduna.
Gwamna Sani ya yaba da shirye-shiryen rage radadin talauci wanda marasa galihu kimani mutum miliyan 1.9 suka amfana a karkashin gwamnatinsa a jihar.
A fagen siyasa, Gwamna Sani ya nuna jin dadinsa da yadda kimanin shugabanni 200,000 daga jam’iyyar adawa ta PDP suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, musamman a Kudancin Kaduna, wanda a cewarsa, wannan wata shaida ce ga ci gaban da gwamnatinsa ta samu wajen tabbatar da adalci, daidaito, da kuma bayyana gaskiya.
Da yake bayani kan yadda za a gudanar da zaben kananan hukumomi, gwamnan ya bayyana kwarin gwiwarsa ga ‘yan takarar jam’iyyar APC, inda ya ba su tabbacin cewa, za su samu cikakken goyon bayansa wajen ciyar da yankunan karkara gaba da kuma tabbatar da daidaiton tattalin arziki a fadin jihar.
Uba sani
Taron ya samu halartar wasu jagorori da shugabannin Jam’iyyar APC a jihar.
Daga cikin mahalarta taron, akwai Mataimakiyar Gwamna, Hajiya Hadiza Sabuwa Balarabe; da Kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Dahiru Liman da sauran masu ruwa da tsaki ciki har da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Muktar Ramalan Yaro.
ADVERTISEMENT
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
Labarai

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Next Post
Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.