ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC

by Sulaiman
2 years ago
Uba sani

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC ya kaddamar da gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC gabanin zaben Shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli da ke tafe a jihar Kaduna a ranar 19 ga watan Oktoba.
Gwamna Sani ya mika tutoci ga ‘yan takarar shugabannin kananan hukumomi a karkashin jam’iyyar APC daga kananan hukumomi 23 da ke jihar.
  • A Shirye Nake Na Rantse Da Alkur’ani Ban Saci Kudin Kaduna Ba – El-Rufai
  • Murnar Ƴanci: Gwamna Fintiri Ya Yafe Wa Fursunoni Biyu
Da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci gangamin yakin neman zaben da za a yi a watan Oktoba, Gwamnan ya bayyana irin gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a muhimman sassa a fadin jihar, musamman ta fuskar farfado da yankunan karkara da samar da ababen more rayuwa.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa, tun bayan hawansa mulki, gwamnatinsa ta ba da fifiko wajen raya karkara, inda ta kaddamar da gina tituna 62 a fadin kananan hukumomi 23.
A bangaren Ilimi, gwamnatin ta gina makarantun sakandire 60. Bugu da kari, an rage adadin yaran da ba sa zuwa makaranta da 300,000 ta hanyar sabin tsarin ilimi da sabuwar gwamnatin ta kirkiro.
Uba sani
Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannin kiwon lafiya, inda ya ce, an kammala inganta manyan cibiyoyin kula da lafiya 9, yayin da ake kan gina wasu sabbi 4, sannan kuma, an samar wa cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko 290 kayayyakin aiki.
Gwamnan ya jaddada cewa, kula da lafiya ba alfarma ba ce, hakki ne ga al’ummar jihar Kaduna.
Gwamna Sani ya yaba da shirye-shiryen rage radadin talauci wanda marasa galihu kimani mutum miliyan 1.9 suka amfana a karkashin gwamnatinsa a jihar.
A fagen siyasa, Gwamna Sani ya nuna jin dadinsa da yadda kimanin shugabanni 200,000 daga jam’iyyar adawa ta PDP suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, musamman a Kudancin Kaduna, wanda a cewarsa, wannan wata shaida ce ga ci gaban da gwamnatinsa ta samu wajen tabbatar da adalci, daidaito, da kuma bayyana gaskiya.
Da yake bayani kan yadda za a gudanar da zaben kananan hukumomi, gwamnan ya bayyana kwarin gwiwarsa ga ‘yan takarar jam’iyyar APC, inda ya ba su tabbacin cewa, za su samu cikakken goyon bayansa wajen ciyar da yankunan karkara gaba da kuma tabbatar da daidaiton tattalin arziki a fadin jihar.
Uba sani
Taron ya samu halartar wasu jagorori da shugabannin Jam’iyyar APC a jihar.
Daga cikin mahalarta taron, akwai Mataimakiyar Gwamna, Hajiya Hadiza Sabuwa Balarabe; da Kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Dahiru Liman da sauran masu ruwa da tsaki ciki har da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Muktar Ramalan Yaro.
Uba sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.