ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC

by Sulaiman
2 years ago
Uba sani

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC ya kaddamar da gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC gabanin zaben Shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli da ke tafe a jihar Kaduna a ranar 19 ga watan Oktoba.
Gwamna Sani ya mika tutoci ga ‘yan takarar shugabannin kananan hukumomi a karkashin jam’iyyar APC daga kananan hukumomi 23 da ke jihar.
  • A Shirye Nake Na Rantse Da Alkur’ani Ban Saci Kudin Kaduna Ba – El-Rufai
  • Murnar Ƴanci: Gwamna Fintiri Ya Yafe Wa Fursunoni Biyu
Da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci gangamin yakin neman zaben da za a yi a watan Oktoba, Gwamnan ya bayyana irin gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a muhimman sassa a fadin jihar, musamman ta fuskar farfado da yankunan karkara da samar da ababen more rayuwa.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa, tun bayan hawansa mulki, gwamnatinsa ta ba da fifiko wajen raya karkara, inda ta kaddamar da gina tituna 62 a fadin kananan hukumomi 23.
A bangaren Ilimi, gwamnatin ta gina makarantun sakandire 60. Bugu da kari, an rage adadin yaran da ba sa zuwa makaranta da 300,000 ta hanyar sabin tsarin ilimi da sabuwar gwamnatin ta kirkiro.
Uba sani
Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannin kiwon lafiya, inda ya ce, an kammala inganta manyan cibiyoyin kula da lafiya 9, yayin da ake kan gina wasu sabbi 4, sannan kuma, an samar wa cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko 290 kayayyakin aiki.
Gwamnan ya jaddada cewa, kula da lafiya ba alfarma ba ce, hakki ne ga al’ummar jihar Kaduna.
Gwamna Sani ya yaba da shirye-shiryen rage radadin talauci wanda marasa galihu kimani mutum miliyan 1.9 suka amfana a karkashin gwamnatinsa a jihar.
A fagen siyasa, Gwamna Sani ya nuna jin dadinsa da yadda kimanin shugabanni 200,000 daga jam’iyyar adawa ta PDP suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, musamman a Kudancin Kaduna, wanda a cewarsa, wannan wata shaida ce ga ci gaban da gwamnatinsa ta samu wajen tabbatar da adalci, daidaito, da kuma bayyana gaskiya.
Da yake bayani kan yadda za a gudanar da zaben kananan hukumomi, gwamnan ya bayyana kwarin gwiwarsa ga ‘yan takarar jam’iyyar APC, inda ya ba su tabbacin cewa, za su samu cikakken goyon bayansa wajen ciyar da yankunan karkara gaba da kuma tabbatar da daidaiton tattalin arziki a fadin jihar.
Uba sani
Taron ya samu halartar wasu jagorori da shugabannin Jam’iyyar APC a jihar.
Daga cikin mahalarta taron, akwai Mataimakiyar Gwamna, Hajiya Hadiza Sabuwa Balarabe; da Kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Dahiru Liman da sauran masu ruwa da tsaki ciki har da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Muktar Ramalan Yaro.
Uba sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

Iniesta Ya Yi Ritaya Daga Buga Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.