• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Bayar Da Kyautar Gwarzon Dan Wasan Afirka A Moroko

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
in Wasanni
0
Za A Bayar Da Kyautar Gwarzon Dan Wasan Afirka A Moroko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF ta sanar da cewa za a gabatar da bikin kyautar gwarazan dan wasan Afrika ta shekara ta 2024 a birnin yawon bude ido na Marrakesh da ke kasar Moroko.

Kuma an tsara za a gudanar da kyautar ne a ranar 16 ga watan Disambar 2024 a cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na D, CAF ta sanar da cewa lokaci ya sake zagayowa domin gudanar da wannan bikin na shekara-shekara.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Wannan ne karo na biyu a jere da ake gudanar da bikin a birnin na Marrakesh, karo na uku kuma da ake yi a kasar Moroko sannan CAF ta ce za ta tabbatar da lokacin da za a fara kyautar ta 2024 da zarar lokaci ya yi.

Wanda ke rike da kambun kyautar ta bangaren maza shi ne dan wasan Najeriya na gaba, Bictor Osimhen sai a bangaren mata kuwa takwararsa da Najariya Asisat Oshoala ce ke rike da kyautar ta shekara ta 2023.

Kyautar tana mayar da hankali ne kan kokarin da ‘yan wasa ke yi a kasarsu da kuma kungiyoyin da suke bugawa kwallo, domin bayar da wannan kyauta mai daraja ta gwarazan Afrika bangaren maza da mata ta shekara.

Labarai Masu Nasaba

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Dabi Alonso Zai Maye Gurbin Ancelotti A Real Madrid

Wasu rahotanni daga kasar Spaniya sun bayyana cewa tuni shugaban gudanar da kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Florentino Perez ya yi umarnin fara shirye-shiryen tarbar mai koyarwa Dabi Alonso a kakar wasa mai zuwa.

Bayanai sun ce Perez a fusace ya ke da yadda Ancelotti ke tafiyar da kungiyar a yanzu haka, duk da zuwan zakakuran dan wasa irinsu Kylian Mbappe na Faransa, wanda ya koma kungiyar daga PSG a farkon wannan kakar.

A cewar rahotannin, hatta ranar Asabar din da ta gabata ya yin wasan hamayya na El Classico anga fushi karara a fuskar Perez bayan ruwan kwallayen da tawagar ta Ancelotti ta sha a hannun babbar abokiyar hamayyarta, Barcelona.

Bayan rawar da Ancelotti ya taka a kakar da ta gabata ne, Perez ya amince da tsawaita kwantiraginsa zuwa shekara ta 2026 sai dai shugaban a yanzu ya fara saka shakku ganin koma bayan da kungiyar ke gani watakila ko saboda yawan shekarun kociyan dan asalin kasar Italiya wanda ya lashe kofin zakarun Turai har guda 3 ga kungiyar.

Baya ga batutuwa masu alaka da raguwar karsashin Real Madrid, Carlo Ancelotti na rikici da mahukuntan kungiyar kan batutuwa da dama ciki har da sabunta kwantiragin Mendy da kungiyar bata so ba amma Ancelotti ya kafe, sai kuma alkawuran kocin game da makomar Arda Guler dan Turkiya, dan wasan da baya samun dama karkashin manajan.

A bangaren mai koyarwa Alonso, duk da cewa tsirarun masu koyarwa ne ka iya cewa a’a ga Real Madrid amma ana ganin abu ne mai wuya kungiyar ta iya shawo kan sa cikin sauki lura da cewa a watan Yunin da ya gabata ne ya sabunta kwantiraginsa kuma kungiyoyi da dama sun nemi aiki da shi amma ya juya musu baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaGwarzoWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Kawo Karshen Mace-mace A Hanyoyinmu

Next Post

An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

Related

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

2 days ago
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

3 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

4 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

5 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

5 days ago
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
Wasanni

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

5 days ago
Next Post
An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

June 5, 2025
Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.