ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Bayar Da Kyautar Gwarzon Dan Wasan Afirka A Moroko

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Gwarzon

Hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF ta sanar da cewa za a gabatar da bikin kyautar gwarazan dan wasan Afrika ta shekara ta 2024 a birnin yawon bude ido na Marrakesh da ke kasar Moroko.

Kuma an tsara za a gudanar da kyautar ne a ranar 16 ga watan Disambar 2024 a cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na D, CAF ta sanar da cewa lokaci ya sake zagayowa domin gudanar da wannan bikin na shekara-shekara.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Wannan ne karo na biyu a jere da ake gudanar da bikin a birnin na Marrakesh, karo na uku kuma da ake yi a kasar Moroko sannan CAF ta ce za ta tabbatar da lokacin da za a fara kyautar ta 2024 da zarar lokaci ya yi.

ADVERTISEMENT

Wanda ke rike da kambun kyautar ta bangaren maza shi ne dan wasan Najeriya na gaba, Bictor Osimhen sai a bangaren mata kuwa takwararsa da Najariya Asisat Oshoala ce ke rike da kyautar ta shekara ta 2023.

Kyautar tana mayar da hankali ne kan kokarin da ‘yan wasa ke yi a kasarsu da kuma kungiyoyin da suke bugawa kwallo, domin bayar da wannan kyauta mai daraja ta gwarazan Afrika bangaren maza da mata ta shekara.

LABARAI MASU NASABA

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

Dabi Alonso Zai Maye Gurbin Ancelotti A Real Madrid

Wasu rahotanni daga kasar Spaniya sun bayyana cewa tuni shugaban gudanar da kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Florentino Perez ya yi umarnin fara shirye-shiryen tarbar mai koyarwa Dabi Alonso a kakar wasa mai zuwa.

Bayanai sun ce Perez a fusace ya ke da yadda Ancelotti ke tafiyar da kungiyar a yanzu haka, duk da zuwan zakakuran dan wasa irinsu Kylian Mbappe na Faransa, wanda ya koma kungiyar daga PSG a farkon wannan kakar.

A cewar rahotannin, hatta ranar Asabar din da ta gabata ya yin wasan hamayya na El Classico anga fushi karara a fuskar Perez bayan ruwan kwallayen da tawagar ta Ancelotti ta sha a hannun babbar abokiyar hamayyarta, Barcelona.

Bayan rawar da Ancelotti ya taka a kakar da ta gabata ne, Perez ya amince da tsawaita kwantiraginsa zuwa shekara ta 2026 sai dai shugaban a yanzu ya fara saka shakku ganin koma bayan da kungiyar ke gani watakila ko saboda yawan shekarun kociyan dan asalin kasar Italiya wanda ya lashe kofin zakarun Turai har guda 3 ga kungiyar.

Baya ga batutuwa masu alaka da raguwar karsashin Real Madrid, Carlo Ancelotti na rikici da mahukuntan kungiyar kan batutuwa da dama ciki har da sabunta kwantiragin Mendy da kungiyar bata so ba amma Ancelotti ya kafe, sai kuma alkawuran kocin game da makomar Arda Guler dan Turkiya, dan wasan da baya samun dama karkashin manajan.

A bangaren mai koyarwa Alonso, duk da cewa tsirarun masu koyarwa ne ka iya cewa a’a ga Real Madrid amma ana ganin abu ne mai wuya kungiyar ta iya shawo kan sa cikin sauki lura da cewa a watan Yunin da ya gabata ne ya sabunta kwantiraginsa kuma kungiyoyi da dama sun nemi aiki da shi amma ya juya musu baya.

Gwarzon
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027
  • Abba Ibrahim Wada
    Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

MASU ALAKA

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?
Wasanni

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi
Wasanni

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Next Post
An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.