ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Bayar Da Kyautar Gwarzon Dan Wasan Afirka A Moroko

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Gwarzon

Hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF ta sanar da cewa za a gabatar da bikin kyautar gwarazan dan wasan Afrika ta shekara ta 2024 a birnin yawon bude ido na Marrakesh da ke kasar Moroko.

Kuma an tsara za a gudanar da kyautar ne a ranar 16 ga watan Disambar 2024 a cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na D, CAF ta sanar da cewa lokaci ya sake zagayowa domin gudanar da wannan bikin na shekara-shekara.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Wannan ne karo na biyu a jere da ake gudanar da bikin a birnin na Marrakesh, karo na uku kuma da ake yi a kasar Moroko sannan CAF ta ce za ta tabbatar da lokacin da za a fara kyautar ta 2024 da zarar lokaci ya yi.

ADVERTISEMENT

Wanda ke rike da kambun kyautar ta bangaren maza shi ne dan wasan Najeriya na gaba, Bictor Osimhen sai a bangaren mata kuwa takwararsa da Najariya Asisat Oshoala ce ke rike da kyautar ta shekara ta 2023.

Kyautar tana mayar da hankali ne kan kokarin da ‘yan wasa ke yi a kasarsu da kuma kungiyoyin da suke bugawa kwallo, domin bayar da wannan kyauta mai daraja ta gwarazan Afrika bangaren maza da mata ta shekara.

LABARAI MASU NASABA

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Dabi Alonso Zai Maye Gurbin Ancelotti A Real Madrid

Wasu rahotanni daga kasar Spaniya sun bayyana cewa tuni shugaban gudanar da kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Florentino Perez ya yi umarnin fara shirye-shiryen tarbar mai koyarwa Dabi Alonso a kakar wasa mai zuwa.

Bayanai sun ce Perez a fusace ya ke da yadda Ancelotti ke tafiyar da kungiyar a yanzu haka, duk da zuwan zakakuran dan wasa irinsu Kylian Mbappe na Faransa, wanda ya koma kungiyar daga PSG a farkon wannan kakar.

A cewar rahotannin, hatta ranar Asabar din da ta gabata ya yin wasan hamayya na El Classico anga fushi karara a fuskar Perez bayan ruwan kwallayen da tawagar ta Ancelotti ta sha a hannun babbar abokiyar hamayyarta, Barcelona.

Bayan rawar da Ancelotti ya taka a kakar da ta gabata ne, Perez ya amince da tsawaita kwantiraginsa zuwa shekara ta 2026 sai dai shugaban a yanzu ya fara saka shakku ganin koma bayan da kungiyar ke gani watakila ko saboda yawan shekarun kociyan dan asalin kasar Italiya wanda ya lashe kofin zakarun Turai har guda 3 ga kungiyar.

Baya ga batutuwa masu alaka da raguwar karsashin Real Madrid, Carlo Ancelotti na rikici da mahukuntan kungiyar kan batutuwa da dama ciki har da sabunta kwantiragin Mendy da kungiyar bata so ba amma Ancelotti ya kafe, sai kuma alkawuran kocin game da makomar Arda Guler dan Turkiya, dan wasan da baya samun dama karkashin manajan.

A bangaren mai koyarwa Alonso, duk da cewa tsirarun masu koyarwa ne ka iya cewa a’a ga Real Madrid amma ana ganin abu ne mai wuya kungiyar ta iya shawo kan sa cikin sauki lura da cewa a watan Yunin da ya gabata ne ya sabunta kwantiraginsa kuma kungiyoyi da dama sun nemi aiki da shi amma ya juya musu baya.

Gwarzon
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke

MASU ALAKA

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
Wasanni

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo
Wasanni

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

An Zargi FIFA Da Kin Biyan Hakkokin ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.