• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Labarai
0
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sanar da cewa za ta fara ba da sufuri kyauta ga ma’aikatan gwamnati, masu ritaya da ɗalibai daga ranar Litinin, 7 ga Yuli, 2025, a ƙarƙashin shirin Kaduna Subsidised Transport Scheme (KSTS).

Darakta Janar na Hukumar Kula da Sufuri ta Jihar Kaduna (KADSTRA), Inuwa Ibrahim, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce za a ba waɗannan rukuni uku damar amfani da motocin kyauta har na tsawon watanni shida.

  • Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Ibrahim ya ƙara da cewa dukkan ɗalibai, ko na makarantar gwamnati ko masu zaman kansu, daga matakin firamare zuwa manyan makarantu, za su amfana da wannan tsari. Ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin kokarin Gwamna Uba Sani na saukaka rayuwa ga ma’aikata, dalibai da tsofaffin da suka yi ritaya daga aiki.6

An bayyana cewa ma’aikatan gwamnati za su sami damar hawa motocin ne ta hanyar nuna katin shaida na aiki tare da lambar NIN domin hana amfani da tsarin ba bisa ƙa’ida ba. Ɗalibai kuwa sai sun kasance cikin cikakken kayan makaranta kafin su hau motar, yayin da jami’an tsaro daga hukumomin da aka amince da su za su iya hawa bayan sun gabatar da shaidarsu ta aiki.

Darakta Janar din ya jaddada cewa za a gudanar da wannan sufuri ne cikin tsari da tsauraran matakan tsaro da bin doka, domin tabbatar da ingantaccen aiki da aminci. Ya buƙaci al’umma su haɗa kai da jami’an sufuri domin cimma nasarar shirin, yana mai cewa motocin farko za su fara zirga-zirga a hanyoyin da aka ware daga ranar Litinin mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊalibaiKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

Next Post

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

1 hour ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

5 hours ago
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

19 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

20 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

1 day ago
Next Post
Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

LABARAI MASU NASABA

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

July 6, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

July 6, 2025
Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

July 6, 2025
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

July 6, 2025
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

July 6, 2025
Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

July 6, 2025
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

July 6, 2025
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

July 6, 2025
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.