• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Za A Ga Alfanun Sauye-sauyen Gwamnati Badi”

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Alfanun

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi tsokaci kan watanni shida da gwamnatinsa ta yi a kan garagar mulki, inda ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa su tsammaci samun sakamako mai kyau daga cikakkun manufofinsa na sauye-sauye da ya aiwatar a shekara mai zuwa.

Ya kuma bakaci a bai wa gwamnatinsa goyon baya kan inganta harkokin tsaro a yankin kudu maso gabas da kudu maso kudu da arewa maso gabas da arewa maso yamma, inda ya ce jami’an tsaro na fatattakar ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga.

  • Majalisar Dattijai Ta Amince Da Naɗin Alkalai 11 A Kotun Ƙoli Da Tinubu Ya Aike Da Su
  • Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Shugaban ya bukaci hukumomin tsaro da su kara himma wajen ganin kasar nan ta kubuta daga ayyukan ta’addanci.

Tinubu ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake kaddamar da sabon rukunin runduna ta shiyyar Inugu na hukumar yaki da yi wa tattalin arziki tu’annati (EFCC) a Inugu.

Ya samu wakilcin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, wanda shi tsohon shugaban hukumar yaki da yi wa tattalin arziki tu’annati ne.

LABARAI MASU NASABA

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

Ya ce, “Da farko, ina kawo gaisuwar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu. Ya ce ya kamata in taya shugaban EFCC, Ola Olukoyede da tawagarsa murna. Na gode da kyakkyawan aiki da kuke yi.

“Ya ce ya kamata in gode wa sojojin Nijeriya da jami’an tsaron ’yansanda da jami’an tsaro na farin kaya (DSS) da sauran su bisa irin kyakkyawan aiki da kuke yi a kasarmu a yau.

“Kowa zai yarda da ni idan na ce abubuwa suna canzawa. A cikin watanni shida na farkon wannan gwamnati, mun fara ganin abubuwan da zai yiwu. Muna kuma so mu kara muku kwarin kwiwa wajen ci gaba da bin wannan hanyar.

“Muna bukatar kasarmu ta yi aiki. Muna bukatar abubuwa don inganta tsarin. Muna son yin abubuwan da suka dace. Kuma shi mai girma shugaban kasa yana kan gaba wajen yin hakan. Al’amura suna canjawa a Nijeriya. A 2024, ku jira ku ga abin da zai faru.”

Ribadu ya tabbatar wa dukkan hukumomin tsaro kudirin shugaban kasa na ba da fifiko ga jin dadinsu, ya kuma yi kira gare su da su yi aiki tare domin samun sakamako mai kyau.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Manyan Labarai

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci
Labarai

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Next Post
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu

Bashin Cikin Gida Ya Karu Da Kashi 134, Ya Kai Naira Tiriliyan 52

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.