• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Za A Ga Alfanun Sauye-sauyen Gwamnati Badi”

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi tsokaci kan watanni shida da gwamnatinsa ta yi a kan garagar mulki, inda ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa su tsammaci samun sakamako mai kyau daga cikakkun manufofinsa na sauye-sauye da ya aiwatar a shekara mai zuwa.

Ya kuma bakaci a bai wa gwamnatinsa goyon baya kan inganta harkokin tsaro a yankin kudu maso gabas da kudu maso kudu da arewa maso gabas da arewa maso yamma, inda ya ce jami’an tsaro na fatattakar ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga.

  • Majalisar Dattijai Ta Amince Da Naɗin Alkalai 11 A Kotun Ƙoli Da Tinubu Ya Aike Da Su
  • Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Shugaban ya bukaci hukumomin tsaro da su kara himma wajen ganin kasar nan ta kubuta daga ayyukan ta’addanci.

Tinubu ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake kaddamar da sabon rukunin runduna ta shiyyar Inugu na hukumar yaki da yi wa tattalin arziki tu’annati (EFCC) a Inugu.

Ya samu wakilcin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, wanda shi tsohon shugaban hukumar yaki da yi wa tattalin arziki tu’annati ne.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ya ce, “Da farko, ina kawo gaisuwar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu. Ya ce ya kamata in taya shugaban EFCC, Ola Olukoyede da tawagarsa murna. Na gode da kyakkyawan aiki da kuke yi.

“Ya ce ya kamata in gode wa sojojin Nijeriya da jami’an tsaron ’yansanda da jami’an tsaro na farin kaya (DSS) da sauran su bisa irin kyakkyawan aiki da kuke yi a kasarmu a yau.

“Kowa zai yarda da ni idan na ce abubuwa suna canzawa. A cikin watanni shida na farkon wannan gwamnati, mun fara ganin abubuwan da zai yiwu. Muna kuma so mu kara muku kwarin kwiwa wajen ci gaba da bin wannan hanyar.

“Muna bukatar kasarmu ta yi aiki. Muna bukatar abubuwa don inganta tsarin. Muna son yin abubuwan da suka dace. Kuma shi mai girma shugaban kasa yana kan gaba wajen yin hakan. Al’amura suna canjawa a Nijeriya. A 2024, ku jira ku ga abin da zai faru.”

Ribadu ya tabbatar wa dukkan hukumomin tsaro kudirin shugaban kasa na ba da fifiko ga jin dadinsu, ya kuma yi kira gare su da su yi aiki tare domin samun sakamako mai kyau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Bashin Cikin Gida Ya Karu Da Kashi 134, Ya Kai Naira Tiriliyan 52

Related

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

2 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

4 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

6 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

7 hours ago
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

18 hours ago
Next Post
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu

Bashin Cikin Gida Ya Karu Da Kashi 134, Ya Kai Naira Tiriliyan 52

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.