• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ce za a kammala aikin titin Kaduna, Zariya zuwa Kano kafin ranar 29 ga watan Mayu.

Ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Raji-Fashola (SAN), ne ya bayyana hakan a ranar Litinin, yayin da ya ke ziyarar duba aikin babbar hanyar.

  • Sin Ta Riga Ta Kasance Muhimmin Bangare A Cikin Ayyukan Kiyaye Zaman Lafiya Na MDD
  • Jami’in IMF: Bunkasuwar Sin Tana Ba Da Gudummawa Ga Kasar Da Ma Daidaiton Harkokin Kudi A Duniya

Bangaren babbar hanyar na daga cikin aikin da ya kai kilomita 375.4 daga Abuja-Kaduna-Zariya-Kano da aka bayar a lokacin mulkin Buhari na farko.

Ya ce za a kammala sashen kuma za a bude shi kafin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka daga mulki a watan Mayu.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa, aikin sake gina hanyar Abuja-Kaduna-Zariya-Kano ya kasu kashi uku.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Fashola ya ce yayin da aka kusa kammala kashi na biyu da na uku wanda ya kai kilomita 210, sashe na daya daga Abuja zuwa Kaduna za a bar wa gwamnati mai jiran gado.

“Sashe na daya (Abuja-Kaduna) zai wuce wa’adin mulkin wannan gwamnati, mun yi asara kusan shekara guda a 2022, saboda aikata laifuka da kuma hakkokin hanya,” in ji shi.

Fashola ya bayyana cewa batutuwan da suka kawo tsaikon aikin sun hada da sake gina gine-gine, da na’urorin lantarki, da kasuwanni.

“Abin da muke bukata shi ne mu hada kai da Ministan Babban Birnin Tarayya, gwamnatocin jihohin Neja da Kaduna, domin dakile ayyukan da suke tafiya cikin sauri da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Haka zalika, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana cewa gadar Neja ta biyu ita ma ta kammala don kaddamar da aikinta.

Ya bayyana shi a matsayin aiki na uku da gwamnatin Buhari ta gada.

Gambari ya yaba wa shugaban kasa bisa yadda ya samar da ayyukan more rayuwa a fadin kasar nan.

Manajan Daraktan Hukumar Kula da Zuba Jari ta Nijeriya, Aminu Umar-Sadiq, ya ce suna da hannu wajen samar da wasu ayyuka.

Ya ce baya ga kudade, yana da muhimmanci a warware matsalolin da suka shafi hakkin hanya da kuma tsaro don ci gaba da ayyukan kamar yadda aka tsara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiBuhariFasholaTitin Kaduna Zuwa Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Riga Ta Kasance Muhimmin Bangare A Cikin Ayyukan Kiyaye Zaman Lafiya Na MDD

Next Post

Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

34 minutes ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

12 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

13 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

14 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

17 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

18 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.