• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ce za a kammala aikin titin Kaduna, Zariya zuwa Kano kafin ranar 29 ga watan Mayu.

Ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Raji-Fashola (SAN), ne ya bayyana hakan a ranar Litinin, yayin da ya ke ziyarar duba aikin babbar hanyar.

  • Sin Ta Riga Ta Kasance Muhimmin Bangare A Cikin Ayyukan Kiyaye Zaman Lafiya Na MDD
  • Jami’in IMF: Bunkasuwar Sin Tana Ba Da Gudummawa Ga Kasar Da Ma Daidaiton Harkokin Kudi A Duniya

Bangaren babbar hanyar na daga cikin aikin da ya kai kilomita 375.4 daga Abuja-Kaduna-Zariya-Kano da aka bayar a lokacin mulkin Buhari na farko.

Ya ce za a kammala sashen kuma za a bude shi kafin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka daga mulki a watan Mayu.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa, aikin sake gina hanyar Abuja-Kaduna-Zariya-Kano ya kasu kashi uku.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Fashola ya ce yayin da aka kusa kammala kashi na biyu da na uku wanda ya kai kilomita 210, sashe na daya daga Abuja zuwa Kaduna za a bar wa gwamnati mai jiran gado.

“Sashe na daya (Abuja-Kaduna) zai wuce wa’adin mulkin wannan gwamnati, mun yi asara kusan shekara guda a 2022, saboda aikata laifuka da kuma hakkokin hanya,” in ji shi.

Fashola ya bayyana cewa batutuwan da suka kawo tsaikon aikin sun hada da sake gina gine-gine, da na’urorin lantarki, da kasuwanni.

“Abin da muke bukata shi ne mu hada kai da Ministan Babban Birnin Tarayya, gwamnatocin jihohin Neja da Kaduna, domin dakile ayyukan da suke tafiya cikin sauri da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Haka zalika, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana cewa gadar Neja ta biyu ita ma ta kammala don kaddamar da aikinta.

Ya bayyana shi a matsayin aiki na uku da gwamnatin Buhari ta gada.

Gambari ya yaba wa shugaban kasa bisa yadda ya samar da ayyukan more rayuwa a fadin kasar nan.

Manajan Daraktan Hukumar Kula da Zuba Jari ta Nijeriya, Aminu Umar-Sadiq, ya ce suna da hannu wajen samar da wasu ayyuka.

Ya ce baya ga kudade, yana da muhimmanci a warware matsalolin da suka shafi hakkin hanya da kuma tsaro don ci gaba da ayyukan kamar yadda aka tsara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiBuhariFasholaTitin Kaduna Zuwa Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Riga Ta Kasance Muhimmin Bangare A Cikin Ayyukan Kiyaye Zaman Lafiya Na MDD

Next Post

Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

1 hour ago
Kano
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

3 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

9 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kano

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.