• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola

by Sadiq
3 years ago
Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce za a kammala aikin titin Kaduna, Zariya zuwa Kano kafin ranar 29 ga watan Mayu.

Ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Raji-Fashola (SAN), ne ya bayyana hakan a ranar Litinin, yayin da ya ke ziyarar duba aikin babbar hanyar.

  • Sin Ta Riga Ta Kasance Muhimmin Bangare A Cikin Ayyukan Kiyaye Zaman Lafiya Na MDD
  • Jami’in IMF: Bunkasuwar Sin Tana Ba Da Gudummawa Ga Kasar Da Ma Daidaiton Harkokin Kudi A Duniya

Bangaren babbar hanyar na daga cikin aikin da ya kai kilomita 375.4 daga Abuja-Kaduna-Zariya-Kano da aka bayar a lokacin mulkin Buhari na farko.

Ya ce za a kammala sashen kuma za a bude shi kafin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka daga mulki a watan Mayu.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa, aikin sake gina hanyar Abuja-Kaduna-Zariya-Kano ya kasu kashi uku.

LABARAI MASU NASABA

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

Fashola ya ce yayin da aka kusa kammala kashi na biyu da na uku wanda ya kai kilomita 210, sashe na daya daga Abuja zuwa Kaduna za a bar wa gwamnati mai jiran gado.

“Sashe na daya (Abuja-Kaduna) zai wuce wa’adin mulkin wannan gwamnati, mun yi asara kusan shekara guda a 2022, saboda aikata laifuka da kuma hakkokin hanya,” in ji shi.

Fashola ya bayyana cewa batutuwan da suka kawo tsaikon aikin sun hada da sake gina gine-gine, da na’urorin lantarki, da kasuwanni.

“Abin da muke bukata shi ne mu hada kai da Ministan Babban Birnin Tarayya, gwamnatocin jihohin Neja da Kaduna, domin dakile ayyukan da suke tafiya cikin sauri da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Haka zalika, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana cewa gadar Neja ta biyu ita ma ta kammala don kaddamar da aikinta.

Ya bayyana shi a matsayin aiki na uku da gwamnatin Buhari ta gada.

Gambari ya yaba wa shugaban kasa bisa yadda ya samar da ayyukan more rayuwa a fadin kasar nan.

Manajan Daraktan Hukumar Kula da Zuba Jari ta Nijeriya, Aminu Umar-Sadiq, ya ce suna da hannu wajen samar da wasu ayyuka.

Ya ce baya ga kudade, yana da muhimmanci a warware matsalolin da suka shafi hakkin hanya da kuma tsaro don ci gaba da ayyukan kamar yadda aka tsara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 
Labarai

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Kano
Labarai

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

Kasar Sin Ta Soki Tsokacin Da Kungiyar G7 Ta Yi Kan Batun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Kano

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.