• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ‘Yantar Da Falasɗinawa Nan Ba Da Jimawa Ba – Fani-Kayode

by Sulaiman
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama Femi Fani-Kayode, ya bayyana fatansa na ganin cewa, nan ba da jimawa ba an kawo karshen kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a Gaza da kuma take hakkin bil adama da Sojojin Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.

 

Mista Fani-Kayode, wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin din da ta gabata a yayin bikin ranar Aqsa na 2024 da kungiyar wayar da kan musulmi ta kasa da kasa ta shirya a Legas, ya danganta fatansa kan yadda duniya ke nuna bacin rai da ya biyo bayan kisan kiyashin.

  • Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Matsawa Isra’ila Ta Dakatar Da Ayyukan Soji A Gaza
  • Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

A cewar rahotanni, an kashe mutane fiye da 40,000 da suka hada da mata da yara a yakin da ake ci gaba da gwabzawa.

 

Labarai Masu Nasaba

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Ya ce: “Wajibi ne a kan mu da duk mutum mai hankali ya yi magana kan wannan barnar ta asarar rayukan al’umma.

 

“Kuma na yi farin ciki cewa, zanga-zangar adawa da mugun aikin Isra’ila tana faruwa a duk faɗin duniya a yau. Tana faruwa a Amurka. Tana faruwa a Turai. Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a nahiyar Afirka, kuma mutane da yawa suna tofa albarkacin bakinsu.

 

“Ireland ta yi Allah wadai da hakan. Belgium ta yi Allah wadai da hakan. Spain ta yi Allah wadai da hakan. Kashi 90 cikin 100 na kasashen Kudancin Amurka sun yi Allah wadai da hakan. Mutane da dama a cikin Faransa sun yi Allah wadai da hakan. Hatta Birtaniya ta rage sayar wa Isra’ila da makamai.

 

“Duniya duka tana yin Allah wadai da aikin Isra’ila. Manyan cibiyoyin karatu a Amurka, kamar Harvard, Yale, Oxford, da Cambridge, sun yi zanga-zangar adawa da abin da ke faruwa a Gaza.

 

“Yadda muke fada, da yadda muke magana kan abin da ke faruwa a Gaza a yau, shi ne irin yadda mutane suka yaki wariyar launin fata a Afirka ta Kudu wanda hakan ya bai wa kasar ‘yanci. Don haka, lokaci ne kadan ya rage al’ummar Falasɗinawa su samu ‘yanci na gaskiya.

 

“Muna yin furucin adawa da aikin Isra’ila a nan ta hanyar yin magana a kullum a kasarmu Nijeriya. Dan adam, a ko ina yake Dan Adam ne, Babu ruwanmu da banbancin addini.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaIsra'ilaLebanon
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Irin Hadin Kai Ne Afirka Ke Bukata?

Next Post

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Related

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

3 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

6 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

7 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

15 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

19 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

1 day ago
Next Post
Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.