• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ‘Yantar Da Falasɗinawa Nan Ba Da Jimawa Ba – Fani-Kayode

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama Femi Fani-Kayode, ya bayyana fatansa na ganin cewa, nan ba da jimawa ba an kawo karshen kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a Gaza da kuma take hakkin bil adama da Sojojin Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.

 

Mista Fani-Kayode, wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin din da ta gabata a yayin bikin ranar Aqsa na 2024 da kungiyar wayar da kan musulmi ta kasa da kasa ta shirya a Legas, ya danganta fatansa kan yadda duniya ke nuna bacin rai da ya biyo bayan kisan kiyashin.

  • Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Matsawa Isra’ila Ta Dakatar Da Ayyukan Soji A Gaza
  • Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

A cewar rahotanni, an kashe mutane fiye da 40,000 da suka hada da mata da yara a yakin da ake ci gaba da gwabzawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

Ya ce: “Wajibi ne a kan mu da duk mutum mai hankali ya yi magana kan wannan barnar ta asarar rayukan al’umma.

 

“Kuma na yi farin ciki cewa, zanga-zangar adawa da mugun aikin Isra’ila tana faruwa a duk faɗin duniya a yau. Tana faruwa a Amurka. Tana faruwa a Turai. Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a nahiyar Afirka, kuma mutane da yawa suna tofa albarkacin bakinsu.

 

“Ireland ta yi Allah wadai da hakan. Belgium ta yi Allah wadai da hakan. Spain ta yi Allah wadai da hakan. Kashi 90 cikin 100 na kasashen Kudancin Amurka sun yi Allah wadai da hakan. Mutane da dama a cikin Faransa sun yi Allah wadai da hakan. Hatta Birtaniya ta rage sayar wa Isra’ila da makamai.

 

“Duniya duka tana yin Allah wadai da aikin Isra’ila. Manyan cibiyoyin karatu a Amurka, kamar Harvard, Yale, Oxford, da Cambridge, sun yi zanga-zangar adawa da abin da ke faruwa a Gaza.

 

“Yadda muke fada, da yadda muke magana kan abin da ke faruwa a Gaza a yau, shi ne irin yadda mutane suka yaki wariyar launin fata a Afirka ta Kudu wanda hakan ya bai wa kasar ‘yanci. Don haka, lokaci ne kadan ya rage al’ummar Falasɗinawa su samu ‘yanci na gaskiya.

 

“Muna yin furucin adawa da aikin Isra’ila a nan ta hanyar yin magana a kullum a kasarmu Nijeriya. Dan adam, a ko ina yake Dan Adam ne, Babu ruwanmu da banbancin addini.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaIsra'ilaLebanon
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Irin Hadin Kai Ne Afirka Ke Bukata?

Next Post

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

20 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

LABARAI MASU NASABA

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.