• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Yi Gaggarumin Taron Bunkasa Noma A Legas

•Obasanjo Da Masana Aikin Gona Za Su Halarta

by Abubakar Abba
1 year ago
Aikin Gona

Tsohon Shugaban Kasar Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo da sauran wasu masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, za su halarci wani gagarumin taro a kan aikin noma da ake kira a turance ‘AgriConnect a 2024’.

Za a shirya wannan taro ne, don tattaunawa a kan yadda za a lalubo mafita wajen bunkasa fannin aikin noma a Nijeriya.

  • Yadda Sha’anin Noman Abarba Ke Taimakawa Kyautata Zaman Rayuwar Mazauna Wasu Kauyuka A Kasar Sin
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Kazalika, taron wanda za a gudanar a ranar 31 ga watan Mayun 2024, zai taimaka wajen hadaka tare da yin amfani da fasahar kere-kere, musamman don magance kalubalen da fannin aikin noma na wannan kasa ke fuskanta.

Har ila yau, taken taron shi ne, ‘Cike gibi ta hanyar yin hadaka tare da amfani da kirkire-kirkiren fasahar zamani, domin sama wa fannin aikin noma alkibla mai dorewa a nan gaba a fadin wannan kasa’.

Bugu da kari, taron na kwana guda, za a gudanar da shi ne a dakin taro na Cibiyar Landmarl event da ke Jihar Legas.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Kazalika, taron zai samu halartar masu ruwa da tsaki daga fannin kimiyya, ‘yan kasuwa a fannin aikin noma, cibiyoyin hada-hadar kudi da za su bayar da gudanunwarsu ga kanana da kuma manyan masu noma, domin samun riba da kuma yadda manoman za su rungumi wannan aiki na noma ta hanyar yin amfani da fasahar zamani tare da kuma ilimantar da su dabarun yin noma na zamani.

Mashiryin taron, Dakta Toyosi Obasanjo; a wata sanarwa da ya bai wa LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, taron zai yi matukar taimakawa wajen cike gibin da ake da shi a wannan fanni na aikin noma da kuma kara karfafa hadaka da masu ruwa da tsaki daban-daban.

A cewarsa, daya daga cikin manufar taron ita ce, samar da dabarun da za su taimaka wajen magance kalubalen da fannin aikin noma na wannan kasa ke fuskanta tare kuma da samar da wadataccen abinci a fadin kasar baki-daya.

Ya sanar da cewa, Tsohon Shugaban Kasa; Cif Olusegun Obasanjo ne zai kasance shugaban wannan taro, wanda kuma sauran wadanda aka gayyata wadanda suka hada da mahukunta daga Bankin Masana’antu na Kasa, Bankin Union, Jakadan Faransa, USAID, IITA da kuma Microsoft, za su gabatar da kasidu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare

Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.