• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ƙalubalanci Ƙarin Kuɗin Kira Da Data A Kotu – NATCOMS  

by Naziru Adam Ibrahim and Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Za Mu Ƙalubalanci Ƙarin Kuɗin Kira Da Data A Kotu – NATCOMS  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin ne gwamnatin Nijeriya ta hannun hukumar sadarwa ta (NCC) ta duba koken kamfanonin sadarwar, inda ta amince musu da su yi ƙarin kuɗin kira da sayen data da kashi 50 cikin 100 sabanin abinda suka bukata.

 

A kwanakin nan Kamfanonin sadarwa a Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar gudanarwar kamfanin MTN, Karl Toriola, sun buƙaci amincewar gwamnatin tarayya kan su yi ƙarin kashi 100 bisa 100 na kuɗin kiran waya da data.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Dalilinsu na neman wannan ƙarin, shi ne tsadar rayuwa, wanda ya ce kamfanin sadarwa a Nijeriya na fuskantar barazanar durƙushewa a sakamakon yadda farashin komai ya yi tashin gauron-zabi kama daga farashin man fetur da farashin kuɗin wuta da sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

A cewar Karl Toriola, a halin yanzu ba batun riba suke ba, sai dai yadda za su ci gaba da kasuwanci, ko a kwanakin baya kungiyar kamfanonin sadarwa ta yi barazanar za a iya samun katsewar sabis ɗin waya a wasu sassa na ƙasar muddin ƙarin bai tabbata ba.

 

Hakan na nufin za a iya samun tangarɗa a fannoni daban-daban da suka shafi tsaro da kiwon lafiya da ilimi da harkokin kasuwanci da sauran al’amuran yau da kullum, kasancewar irin tasirin da kafafen sadarwa ke da shi a rayuwar al’umma.

 

Wannan ta ƙaddamar ƙarin dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa game da hauhawar farashi a sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnatin Nijeriya, wanda ake alaƙanta su da cire tallafin man fetur.

 

Shugaban ƙungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta NATCOMS, Deolu Ogunbanjo, ya ce hukumar NCC ba ta tuntuɓesu ba game da ƙarin kashi 50 ciki 100 na farashin kuɗin waya da datan da ta yi.

 

A cewarsa suna sane da ƙalubalen da kamfanonin sadarwa ke fuskanta, tare da bayar da shawarar ƙarin kashi 5 ko 10 cikin 100, ya kuma shaida cewa matakin NCC na ƙarin abu ne da ba za su lamunta ba, inda ya sha alwashin ƙalubalantar ƙarin ƙudin a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Trump

Next Post

Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

3 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

6 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

7 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

12 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

14 hours ago
Next Post
Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.