• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ceto Zamfara, In Ji Atiku Yayin Da Ya Amshi Baƙuncin Dauda Lawal

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Za Mu Ceto Zamfara, In Ji Atiku Yayin Da Ya Amshi Baƙuncin Dauda Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar ya jaddadawa Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal cewa zai yi aiki tuƙuru wurin ganin jam’iyyar PDP ta lashe zaɓen 2023 a Jihar da ma ƙasa bakidaya.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana haka ne jiya laraba a gidansa dake Abuja, yayin da Dauda Lawal ya jagoranci tawagar ‘ya’yan PDP na Jihar Zamfara tare da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa da suka sauka sheƙa daga APC zuwa PDP.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Abdulmalik Tanko Hukuncin Kisa

Atiku ya ce, hanya daya ce za a iya bi wurin ceto Zamfara, shi ne ta hanyar korar APC daga mulki.
“Ba za mu samar da nagartacciyar rayuwa ga jama’a ba har sai mun tabbata mun kori APC, wanda kuma hakan na buƙatan hadin kai.
“Babban abin da mutanen Zamfara ke buƙata a yanzu shi ne zaman lafiya. A samar da tsaro a gonaki, a samar da ayyukan yi. Idan aka yi haka, za a samu inganci a komi na rayuwa” Inji shi

Tun farko a jawabinsa, dan takarar gwamna na PDP a Zamfara, Dr. Dauda Lawal ya bayyana dalilin wannan ziyara a matsayin gaisuwa tare da gabatar da jiga-jigan ‘yan siyasar da suka sauya sheƙa daga APC zuwa PDP. Haka nan kuma don taya murna ga Atiku bisa nasarar da ya samu a zaben fidda gwanin PDP wanda aka yi kwanakin baya.

Lawal ya ce, ‘yan Nijeriya sun gaji da APC, a shirye suke da su zabi PDP a matakin jihohi da ma tarayya. “Samun waɗannan manyan ‘yan siyasa su sauya sheka daga APC zuwa garemu, ba ƙaramar nasara ba ce ga PDP”. Inji shi.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Daga cikin jiga-jigan da suka sauya shekan daga APC zuwa PDP akwai Alhaji Salihu Mai Buhu Gummi, Alhaji Sahabi Liman Kaura, Alhaji Illili Bakura, Engr. Garba Ahmad Yandi, Hon. Ikra Bilbis, Dr. Na’Allah Isa Mayana, Hon. Mukhtar Lugga da sauransu.

Kafin kammala ziyarar, Dauda Lawal ya gabatarwa da Atiku da kyautar rigar saka a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da Zamfara ta shahara da su a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Abdulmalik Tanko Hukuncin Kisa

Next Post

Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

13 hours ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

1 day ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

4 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

2 weeks ago
Next Post
Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.