ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ceto Zamfara, In Ji Atiku Yayin Da Ya Amshi Baƙuncin Dauda Lawal

by Bello Hamza
4 years ago
Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar ya jaddadawa Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal cewa zai yi aiki tuƙuru wurin ganin jam’iyyar PDP ta lashe zaɓen 2023 a Jihar da ma ƙasa bakidaya.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana haka ne jiya laraba a gidansa dake Abuja, yayin da Dauda Lawal ya jagoranci tawagar ‘ya’yan PDP na Jihar Zamfara tare da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa da suka sauka sheƙa daga APC zuwa PDP.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Abdulmalik Tanko Hukuncin Kisa

Atiku ya ce, hanya daya ce za a iya bi wurin ceto Zamfara, shi ne ta hanyar korar APC daga mulki.
“Ba za mu samar da nagartacciyar rayuwa ga jama’a ba har sai mun tabbata mun kori APC, wanda kuma hakan na buƙatan hadin kai.
“Babban abin da mutanen Zamfara ke buƙata a yanzu shi ne zaman lafiya. A samar da tsaro a gonaki, a samar da ayyukan yi. Idan aka yi haka, za a samu inganci a komi na rayuwa” Inji shi

ADVERTISEMENT

Tun farko a jawabinsa, dan takarar gwamna na PDP a Zamfara, Dr. Dauda Lawal ya bayyana dalilin wannan ziyara a matsayin gaisuwa tare da gabatar da jiga-jigan ‘yan siyasar da suka sauya sheƙa daga APC zuwa PDP. Haka nan kuma don taya murna ga Atiku bisa nasarar da ya samu a zaben fidda gwanin PDP wanda aka yi kwanakin baya.

Lawal ya ce, ‘yan Nijeriya sun gaji da APC, a shirye suke da su zabi PDP a matakin jihohi da ma tarayya. “Samun waɗannan manyan ‘yan siyasa su sauya sheka daga APC zuwa garemu, ba ƙaramar nasara ba ce ga PDP”. Inji shi.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Daga cikin jiga-jigan da suka sauya shekan daga APC zuwa PDP akwai Alhaji Salihu Mai Buhu Gummi, Alhaji Sahabi Liman Kaura, Alhaji Illili Bakura, Engr. Garba Ahmad Yandi, Hon. Ikra Bilbis, Dr. Na’Allah Isa Mayana, Hon. Mukhtar Lugga da sauransu.

Kafin kammala ziyarar, Dauda Lawal ya gabatarwa da Atiku da kyautar rigar saka a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da Zamfara ta shahara da su a baya.

Atiku
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
Next Post
Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.