Babban kwamandan rundunar Hisba ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana aniyar hukumarsa ta yin aiki tare da sahihiyar kungiyar Mahaddata Alkur’ani ta ƙasa.
Shehin Malamin ya bayyana haka ne a lokacin da shugaban Majalisar Mahaddata Alkur’ani na kasa, Goni Sunusi Abubakar wanda ya samu rakiyar shugaban kungiyar reshen Jihar Kano, Gwani Laminu Mahmud Salga suka kai masa ziyara a ofishinsa.
- NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano
- Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna
Da yake tsokaci kan korafin da shugaban ya gabatar cewar wani dan Hisba na yin sojan gona da sunan Majalisar Mahaddata Alkur’ani kan shi ne aka zaba a matsayin shugaban kungiyar Jihar Kano, Daurawa cewa mutumin ya zo da takardar cewa shi ne shugaban kungiyar na Jihar Kano, wanda kuma ya bukaci a sa masa albarka.
Don haka sai Daurawa ya tabbatar wa da shugabannin Majalisar Mahaddatan cewar za su gudanar da bincike, domin ba zai yi wu a ci gaba da irin wannan a hukumar ta Hisba ba, daga nan sai ya taya shugabannin majalisar murna tare da alkawarin yin aiki da sahihiyar kungiyar mahaddatan kamar yadda aka gani a lokacin rabon tallafin shinkafar da Gwamnatin Kano ta bayar.
Da yake gabatar da jawabinsa, shugaban Majalisar Mahaddata Alkur’ani na kasa, Goni Sunusi Abubakar ya bayyana matukar damuwa bisa yadda wani mutum ke amfani da sunan wannan kungiya yake bayyana kansa a mtsayin shugaban kungiyar na Jihar Kano.
A lokacin ziyarar, Sheikh Daurawa tare da alkalin kotun hukumar ta Hisba ne suka karbi tawagar shugaban majalisar mahaddatan na kasa, wanda ya samu rakiyar Gwani Laminu Mahmud Salga, Gwani Imam Nazafi Abubakar Gwani Sabo Mai Rigar fata, Gwani Rabi’u Sulaiman Tarauni da Abdullahi Muhammad Sheka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp