• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Kotu Ta Hukunta Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari – Fintiri

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Fintiri

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, na jihar Adamawa, ya tabbatar wa al’ummar jihar kudurin da ya rataya a wuyan gwamnatinsa na ganin ta gurfanar da mutanen da suka hada baki,l da dakatacce kwamishinan hukumar zabe ta kasa (INEC) a jihar, Hudu Yunusa Ari, kan rawar da ya taka a babban zaben 2023.

Fintiri, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yiwa jama’ar jihar jawabi a ranar Litinin, ya ce “mu na iya mu kare tsarin zabenmu da dimokuradiyya daga cin zarafin da bai kamata ba.

  • Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta
  • Bikin Bazara Da Ke Fadada A Duniya Alama Ce Ta Mu’amala Da Fahimtar Juna Tsakanin Wayewar Kan Kasar Sin Da Wayewar Kai Daban-Daban

“Ita kanta kotun Koli a cikin hukuncinta ta yi Allah-wadai da matakin da Hudu Ari ya dauka, ta ce matsayin wani aiki ne na ‘rashin hankali da aikata laifuka’ wanda ya jefa harkar dimokradiyya cikin kunya da dimauta” inji gwamnan.

Haka kuma, gwamna Fintiri, ya nuna gamsuwa da yadda alkalai a matakai daban-daban na kotuna suka jajirce wajen warware rudun da aka kawo a matakai daban-daban tare da fitar da hukuncin da ya dace da al’ummar jihar Adamawa.

Ya ce “hukuncin da kotun koli na ranar 31/01/2024, ya kawo karshen duk wata hayaniyar zaben 2023 a Adamawa, kwanakin karya da yaudara sun kare, lokacin farfagandar karya da maganganun son zuciya sun shude.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

“Dole na yabawa hukumar zabe INEC da ta tsaya tsayin daka ta kare mutunci da kimarta ta gujewa son zuciya, lokacin da Kwamishina Hudu Ari, ya aikata son zuciya da rashin bin ka’idar doka” inji Fintiri.

Gwamna Ahmadu Fintiri, ya ce duk da yanzu ba lokacin takara ba ne, amma jihar Adamawa jiha ce ta jam’iyyar PDP, kamar yadda aka gani lokacin zabuka da kuma a yadda ta kasance a kotuna, an lura da yadda mutanen suka yi magana da katunan zabe.

“Shaidar hakan ita ce sabuwar nasarar da PDP ta samu a zaben dan majalisar dokokin jiha mai wakiltar mazabar karamar hukumar Mayo-Belwa, mu na kara godiya ga masu kada kuri’a da suka kara sanya nasara a kan hukuncin da kotun koli ta yanke” ya jaddada.

Gwamna Ahmadu Fintiri, ya kuma baiwa jama’ar jihar tabbacin gwamnatinsa za ta ci gaba da musu hidima, tsare-tsare da kyautata rayuwa, ilimi kyauta, samar da kiwon lafiya, kayayyakin more rayuwa a birane da karkara, karfafa mata da matasa da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
Next Post
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.