• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabe Gwamna: PDP Ta Nemi Hadakar Wasu Jam’iyyu Domin Kayar Da APC A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Zabe Gwamna: PDP Ta Nemi Hadakar Wasu Jam’iyyu Domin Kayar Da APC A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da ake shirin gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a ranar 11 ga watan Maris 2023, jam’iyyar PDP a Jihar Kaduna na neman hadin gwiwa da sauran jam’iyyun siyasar jihar domin kayar da jam’iyyar APC mai mulki.

Idan za a tuna jam’iyyar PDP ta lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata, da kujeru uku na Sanata da kujerun majalisar wakilai da dama a Jihar Kaduna.

  • Kamfanin Ericsson: Kamfanonin Sadarwa Na Kasar Sin Sun Gaggauta Rungumar Fasahar 5G
  • Wani Bikin Kaddamarwa Mai Muhimmanci

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Hon. Felix Hassan Hyet, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a sakatariyar jam’iyyar da ke Kaduna.

Yayin da yake yabawa al’ummar jihar bisa gagarumin goyon bayan da suka nuna a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya na kananan hukumomi 23, Hon. Hyet ya nemi karin goyon baya a lokacin zaben gwamna da ke tafe.

A cewarsa, kayen da jam’iyyar APC mai mulki ta sha a jihar alama ce ta kin amincewa da gwamnatin APC a Jihar Kaduna gaba daya da mutanen jihar suka yi.

Labarai Masu Nasaba

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

“Ina mika godiya ta ga mutanen Jihar Kaduna da suka fito rumfunan zabe domin zaben jam’iyyar PDP, ina mai alfahari da cewa an nuna tasirin da yakinin al’ummar Jihar Kaduna ta hanyar sakamakon zaben.

“A karon farko a tarihi, PDP ta lashe kujerun sanatoci uku, da kuma mazabu 10 daga cikin 16 na tarayya na jihar, fiye da zaben 2019.”

Hyet ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP a jihar ba ta bar wani abu ba don tabbatar da cewa PDP ta yi nasara a zabe mai zuwa yayin da ya jaddada cewa za su hada kai da sauran jam’iyyu don cikar burinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKadunaPDPZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Ericsson: Kamfanonin Sadarwa Na Kasar Sin Sun Gaggauta Rungumar Fasahar 5G

Next Post

Shugabannin Sin Da Kodibwa Sun Aikewa Juna Sakon Taya Murna

Related

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle
Labarai

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

1 hour ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

2 hours ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

16 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

18 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

19 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

20 hours ago
Next Post
Shugabannin Sin Da Kodibwa Sun Aikewa Juna Sakon Taya Murna

Shugabannin Sin Da Kodibwa Sun Aikewa Juna Sakon Taya Murna

LABARAI MASU NASABA

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.