• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon zabukan da ya gabata da kuma kararrakin zabe da aka shigar a gaban kotu da ba a taba yin irinsa ba, ya kara sanya shakku ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan gudanar da sa-hihin zabe na gaskiya da adalci.

Kodayake dama, tun dawo da mulki ga gwamnatin farar hula a shekarar 1999, ake shiga kotu kan kararrakin zabe, amma a zaben bana, duba da adadin kararrakin zabe da ke gaban kotun daukaka kararrakin zabe, lamarin na da ban tsoro.

  • Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure
  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina

A zaben bana, 2023, an gudanar da zabe a kujerun siyasa daban-daban har 1,280 tun daga kan kujerar shugaban kasa, ‘yan majalisar dattijai 109, majalisar wakilai ta tarayya 360, kujeru 782 na majalisar waki-lai a fadin jihohi 28 da kuma kujerun gwamnoni 28.

Cikin jimillar adadin, an shigar da kararraki 1,209 a gaban alkalai domin yanke hukunci, kamar yadda shugabar kotun daukaka kara (PCA), Mai shari’a Monica Dongban-mensem ta bayyana a lokacin bikin fara shekarar shari’a ta 2023/2024 a Abuja. Wannan ya nuna cewa, kashi 94.453 cikin 100 na kujerun da aka fafata, suna gaban alkalai.

Kujeru 71 ne kacal cikin 1,280 da aka fafata a zaben ba a garzaya kotu ba. Ya nuna kashi 5.547 cikin 100 kenan.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

A watan Nuwamban da ya gabata, shugaban hukumar INEC, Mahmood Yakubu, ya koka kan yadda shari’o’i sama da 600 suke gaban hukumar gabanin zabe a kotuna da dama a fadin tarayyar Nijeriya, kamar yadda jaridar the guardian ta rahoto.

Mahmood ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karawa juna sani ga alkalai sama da 300 da za su gudanar da shari’o’i kan rikicin zabe.

Ya bayyana cewa shari’o’in da ke gaban hukumar zaben sun shafi yadda jam’iyyun siyasa ke gudanar da zaben fidda gwani, yanzun da aka kammala zabe, shari’o’in sun taso, yanzun INEC za ta yi shari’a kusan 1,209, tunda yawanci masu shigar da kara, sun shigar da INEC a cikin kokensu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKotun Daukaka Kara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kashim Shettima: Kasar Sin Ta Kasance Mai Kaunar Zaman Lafiya Da Bunkasar Arzikin Duniya  

Next Post

Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

4 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

5 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

8 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

9 hours ago
Next Post
Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.