• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC

by Sulaiman
2 years ago
inec

Sakamakon zabukan da ya gabata da kuma kararrakin zabe da aka shigar a gaban kotu da ba a taba yin irinsa ba, ya kara sanya shakku ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan gudanar da sa-hihin zabe na gaskiya da adalci.

Kodayake dama, tun dawo da mulki ga gwamnatin farar hula a shekarar 1999, ake shiga kotu kan kararrakin zabe, amma a zaben bana, duba da adadin kararrakin zabe da ke gaban kotun daukaka kararrakin zabe, lamarin na da ban tsoro.

  • Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure
  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina

A zaben bana, 2023, an gudanar da zabe a kujerun siyasa daban-daban har 1,280 tun daga kan kujerar shugaban kasa, ‘yan majalisar dattijai 109, majalisar wakilai ta tarayya 360, kujeru 782 na majalisar waki-lai a fadin jihohi 28 da kuma kujerun gwamnoni 28.

Cikin jimillar adadin, an shigar da kararraki 1,209 a gaban alkalai domin yanke hukunci, kamar yadda shugabar kotun daukaka kara (PCA), Mai shari’a Monica Dongban-mensem ta bayyana a lokacin bikin fara shekarar shari’a ta 2023/2024 a Abuja. Wannan ya nuna cewa, kashi 94.453 cikin 100 na kujerun da aka fafata, suna gaban alkalai.

Kujeru 71 ne kacal cikin 1,280 da aka fafata a zaben ba a garzaya kotu ba. Ya nuna kashi 5.547 cikin 100 kenan.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

A watan Nuwamban da ya gabata, shugaban hukumar INEC, Mahmood Yakubu, ya koka kan yadda shari’o’i sama da 600 suke gaban hukumar gabanin zabe a kotuna da dama a fadin tarayyar Nijeriya, kamar yadda jaridar the guardian ta rahoto.

Mahmood ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karawa juna sani ga alkalai sama da 300 da za su gudanar da shari’o’i kan rikicin zabe.

Ya bayyana cewa shari’o’in da ke gaban hukumar zaben sun shafi yadda jam’iyyun siyasa ke gudanar da zaben fidda gwani, yanzun da aka kammala zabe, shari’o’in sun taso, yanzun INEC za ta yi shari’a kusan 1,209, tunda yawanci masu shigar da kara, sun shigar da INEC a cikin kokensu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben 2023
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2023

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.