ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fidda-Gwanin APC: A. A Jinjiri Ya Maka Bashir Machina Kotu

by Muhammad Maitela
4 years ago
Machina

Ga dukan alamu zaben fidda-gwani da jam’iyyar APC na Sanatan Arewacin Yobe ya bar baya da kura, wanda ya jawo a ranar Juma’a daya daga cikin ‘yan takarar, Abubakar Abubakar Jinjiri, ke kalubalantar nasarar da Bashir Sheriff Machina ya samu zuwa kotu.

Hon. Machina wanda ya lashe zaben da kuri’u 289 a zaben, wanda kuma yake sa-toka sa-katsi tsakanin sa da shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan.

  • Ya Yi Yunkurin Arcewa Bayan Daba Wa Mai Ciki Wuka Ta Mutu
  • Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

Haka zalika, bayan da Lawan ya sha kasa a zaben fidda-gwani na shugaban kasa da APC ta gudanar, ya gamu da turjiyar Machina bisa kin janye masa ya ci gaba da jan zarensa a kan kujerar Sanatan Arewacin Yobe, duk da goyon bayan da yake samu daga uwar jam’iyyar APC ta kasa.

ADVERTISEMENT

A. A Jinjiri yana daga cikin jerin ‘yan takarar da suka mika sunayensu domin kalubalantar zaben fidda-gwani a jihar Yobe, a gaban mai shari’a Fadima Murtala Aminu ta Babbar Kotun Tarayya, da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Da yake zanta wa da manema labarai a gaban kotun, lauyan mai kara, Barists Usman Lukman Nuhu, ya bayyana cewa wanda yake wakilta ya na kalubalantar Machina, tare da uwar jam’iyyar APC ta kasa da ta jihat Yobe, hadi da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), bisa rashin sanya sunan shi a cikin yan takara.

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

Ya kara da cewa, an hana Jinjiri ya shiga zaben fidda-gwani na Sanatan Arewacin Yobe, duk da kuwa yadda ya halarci wajen da aka gudanar da shi.

“Kuma na yi imani cewa kuna da kofi na takardar sakamakon zaben fidda-gwanin, wanda da kanku na san kun tabbatar babu sunan wanda nake bai wa kariya a takardar sakamakon zaben. ” in ji shi.

Har wa yau, ya ce kin saka sunan dan takara abu ne wanda ya saba wa dokar kundin tsarin mulki ta sashe na (84) da karamin sashe na (3 da 4) na dokokin zabe.

Bugu da kari, akwai kararrakin zaben fidda-gwani guda bakwai wadanda ke kalubalantar sakamakon zaben fidda-gwanin da jam’iyyar APC da ta gudanar.

Haka kuma, mai shari’ar ta ayyana ranar 21 ga watan July 21, 2022 a matsayin lokacin fara shari’ar.

Machina
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
Siyasa

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
Siyasa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Next Post
APP Za Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Rashin Takardun Makaranta

APP Za Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Rashin Takardun Makaranta

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.