• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Edo

Zaben fid da gwani na jam’iyyar APC na kokarin fitar da dan takarar gwamna a zaben gwamnan Jihar Edo da zai gudana ranar 21 ga Satumba, ya bar baya da kura, inda a yanzu haka ‘yan takara uku ne ke ikirarin sun yi nasara.

Tun da farko dai, shugaban kwamitin zaben fitar da gwani na APC, Gwamna Hope Uzodinma ya ayyana dan majalisar wakilai, Dennis Idahosa a matsayin wanda ya yi nasara a Otel din Protea da ke Benin, yayin da babban jami’in da ke kula da zaben, Dakta Stanley Ugboaja ya bayyana Sanata Mondaya Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben a gidan Fasto Osagie Ize-lyamu.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Haka zalika, jami’an da suka kula da zaben fitar da gwanin na kanana hukumomi su ayyana Anamero Sundaya Dekeri a matsayin wanda ya yi nasara.

Mai magana da yawun jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi, Ojo Babatunde, ya sanar da sakamakon zaben ne a daren Asabar, inda ya ce Dekeri wanda ya kasance dan majalisa da ke wakiltar Etsaro a zauren majalisar wakilan Nijeriya, ya samu kuri’u 25,384, wanda ya doke abokin takaransa da ke kusa da shi, Dennis Idahosa da kuri’u 14,127.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na APC, Emmanuel Godwin ya bayyana cewa Gwamna Uzodinma bai da hurumin daukan nauyin da ya rataya a kan jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

Da yake mayar da martani kan wannan dambarwar, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya dage cewa bisa doka kwamitin da gwamna Uzodinma ke jagoranta shi kadai ne ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fitar da gwani  na APC  Jihar Edo.

Sakataren yada labarai na APC, Felid Morka ya bayyana cewa mutane su yi watsi da duk wani sakamakon da bai cika ka’ida ba.

“Kwamitin gudanarwa na kasa na wannan babbar jam’iyyarmu ya jawo hankalin kan sanar da sakamakon zaben fitar da gwani na APC a Jihar Edo, wanda wasu wadanda ba su da ikon yin haka suke ta yadawa a gidajen talabijin da rediyo da kuma kafafen sada zumunta.

“Muna sanar da cewa kwamitin da Gwamna Hope Uzodinma yake jagoranta ne kadai ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fid da gwani na APC a Jihar Edo bisa tsarin doka.

“Muna kira da ‘ya’yan jam’iyyarmu na jihar da kuma sauran mutane cewa su yi watsi da duk wata sanarwa da ba ta cika ka’idar doka ba,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa dai, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya kafa kwamitin da zai jagoranta zaben fitar da gwani karkashin shugabancin Gwamna Uzodinma a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce, “Duk abin da wannan kwamitin ta zantar, to ‘yan takara suna da damar daukaka kara. Domin haka ne ma muke da kwamitin daukaka kara wanda ya kasance kamar kotun koli.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Babban Jami'in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025
Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.