ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Edo

Zaben fid da gwani na jam’iyyar APC na kokarin fitar da dan takarar gwamna a zaben gwamnan Jihar Edo da zai gudana ranar 21 ga Satumba, ya bar baya da kura, inda a yanzu haka ‘yan takara uku ne ke ikirarin sun yi nasara.

Tun da farko dai, shugaban kwamitin zaben fitar da gwani na APC, Gwamna Hope Uzodinma ya ayyana dan majalisar wakilai, Dennis Idahosa a matsayin wanda ya yi nasara a Otel din Protea da ke Benin, yayin da babban jami’in da ke kula da zaben, Dakta Stanley Ugboaja ya bayyana Sanata Mondaya Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben a gidan Fasto Osagie Ize-lyamu.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Haka zalika, jami’an da suka kula da zaben fitar da gwanin na kanana hukumomi su ayyana Anamero Sundaya Dekeri a matsayin wanda ya yi nasara.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi, Ojo Babatunde, ya sanar da sakamakon zaben ne a daren Asabar, inda ya ce Dekeri wanda ya kasance dan majalisa da ke wakiltar Etsaro a zauren majalisar wakilan Nijeriya, ya samu kuri’u 25,384, wanda ya doke abokin takaransa da ke kusa da shi, Dennis Idahosa da kuri’u 14,127.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na APC, Emmanuel Godwin ya bayyana cewa Gwamna Uzodinma bai da hurumin daukan nauyin da ya rataya a kan jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Da yake mayar da martani kan wannan dambarwar, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya dage cewa bisa doka kwamitin da gwamna Uzodinma ke jagoranta shi kadai ne ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fitar da gwani  na APC  Jihar Edo.

Sakataren yada labarai na APC, Felid Morka ya bayyana cewa mutane su yi watsi da duk wani sakamakon da bai cika ka’ida ba.

“Kwamitin gudanarwa na kasa na wannan babbar jam’iyyarmu ya jawo hankalin kan sanar da sakamakon zaben fitar da gwani na APC a Jihar Edo, wanda wasu wadanda ba su da ikon yin haka suke ta yadawa a gidajen talabijin da rediyo da kuma kafafen sada zumunta.

“Muna sanar da cewa kwamitin da Gwamna Hope Uzodinma yake jagoranta ne kadai ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fid da gwani na APC a Jihar Edo bisa tsarin doka.

“Muna kira da ‘ya’yan jam’iyyarmu na jihar da kuma sauran mutane cewa su yi watsi da duk wata sanarwa da ba ta cika ka’idar doka ba,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa dai, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya kafa kwamitin da zai jagoranta zaben fitar da gwani karkashin shugabancin Gwamna Uzodinma a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce, “Duk abin da wannan kwamitin ta zantar, to ‘yan takara suna da damar daukaka kara. Domin haka ne ma muke da kwamitin daukaka kara wanda ya kasance kamar kotun koli.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Babban Jami'in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.