• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Ghana: Sojin Kasar Sun Yi Damarar Samar Da Zaman Lafiya

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Ghana

Babban Hafsan Sojin Kasar Ghana, Manjo Janar Bismarck Kwasi Onwona, ya gargadi sojojin kasar da su kaucewa yaudarar ‘yan siyasa kana kar su karkata ta wani bangare siyasa gabanin babban zabe na watan Disamban shekarar 2024.

Ya kuma jaddada bukatar jami’an soji su nuna kwarewa ba tare da shiga harkokin siyasa ba a daidai lokacin da kasar ke tunkarar wannan lokacin mai muhimmanci.

  • Yadda Ake Kosan Filantan
  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya

Da yake jawabi a kan rawar da sojojin ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya a lokacin zaben, Manjo Janar Onwona ya jaddada aniyar rundunar sojin ta ci gaba da tabbatar da kwarewa.

Ya yi kira ga daukacin jami’an soja da su mai da hankali kan ayyukansu domin tabbatar da cewa an gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali da lumana, yana mai tabbatar wa ‘yan kasar Ghana a shirye sojojin suke wajen kare kasar a lokacin zabe.

A jawabinsa, Manjo Janar Onwona ya kuma yi kira ga kafafen yada labarai da su yi aiki yadda ya kamata, inda ya bukace su da su guji yada labaran karya da na kirkira.

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Ya kuma yi gargadin cewa bada rahotanni marasa tushe na iya yin barazana ga zaman lafiyar kasar da ta da fitina, musamman a lokacin zabe mai matukar muhimmanci.

“Ban ware wani rukuni na mutane ba. Abin da nake nufi shi ne, kada wani ya yaudare su; kama daga ‘yan siyasa, ‘yan jarida, ko kuma ‘yan kasuwa”.

“Mu ba ‘yan siyasa ba ne, aikinmu shi ne kare Kundin Tsarin Mulki. Don haka, ina magana ne ga kowa da kowa da ke da niyyar yaudarar kowane jami’in Sojojin ta hanyar da ba ta dace ba, ”in ji shi.

Shugaban rundunar sojin ya yi wannan jawabi ne a lokacin kaddamar da wani sabon wurin kwana ga jami’an da ke babban ofishin rundunar da ke Kumasi.

An gudanar da aikin ne da nufin inganta rayuwar jami’an soji, wanda ke karkashin kulawar Birgediya Janar Michael Kwadwo Opoku, babban kwamandan runduna ta tsakiya.

Ana sa ran sabon ginin da aka kaddamar zai inganta jin dadin jami’an soji da ke yankin, a daidai lokacin da rundunar ke shirin tallafawa kokarin kasar na gudanar da zabe cikin nasara da lumana a cikin watan Disamba.

A wani labarin kuma, Amurka za ta hana wasu ‘yan ghana biza. Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da Ghana ke shirin gudanar da zaben shugaban kasa a watan Disambar 2024.

Amurka ta sanar da wani tsarin takaita biza ga mutanen da hukumomin Washington ke ganin suna da alhakin haifar da cikas ga tsarin dimokradiyya a Ghana, gabanin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar da za a gudanar a watan Disamba a kasar wacce ke Yammacin Afirka.

“Wannan tsarin takaita biza zai shafi wasu mutanen da ke cin dunduniyar tsarin dimokradiyya ne kawai kuma ba ana nufin za ta shafi al’ummar Ghana ba ko kuma gwamnatin Ghana,” in ji Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a ranar Litinin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Next Post
Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta ‘Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta 'Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

LABARAI MASU NASABA

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.