• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Ghana: Sojin Kasar Sun Yi Damarar Samar Da Zaman Lafiya

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kasashen Ketare
0
Zaben Ghana: Sojin Kasar Sun Yi Damarar Samar Da Zaman Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan Sojin Kasar Ghana, Manjo Janar Bismarck Kwasi Onwona, ya gargadi sojojin kasar da su kaucewa yaudarar ‘yan siyasa kana kar su karkata ta wani bangare siyasa gabanin babban zabe na watan Disamban shekarar 2024.

Ya kuma jaddada bukatar jami’an soji su nuna kwarewa ba tare da shiga harkokin siyasa ba a daidai lokacin da kasar ke tunkarar wannan lokacin mai muhimmanci.

  • Yadda Ake Kosan Filantan
  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya

Da yake jawabi a kan rawar da sojojin ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya a lokacin zaben, Manjo Janar Onwona ya jaddada aniyar rundunar sojin ta ci gaba da tabbatar da kwarewa.

Ya yi kira ga daukacin jami’an soja da su mai da hankali kan ayyukansu domin tabbatar da cewa an gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali da lumana, yana mai tabbatar wa ‘yan kasar Ghana a shirye sojojin suke wajen kare kasar a lokacin zabe.

A jawabinsa, Manjo Janar Onwona ya kuma yi kira ga kafafen yada labarai da su yi aiki yadda ya kamata, inda ya bukace su da su guji yada labaran karya da na kirkira.

Labarai Masu Nasaba

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Ya kuma yi gargadin cewa bada rahotanni marasa tushe na iya yin barazana ga zaman lafiyar kasar da ta da fitina, musamman a lokacin zabe mai matukar muhimmanci.

“Ban ware wani rukuni na mutane ba. Abin da nake nufi shi ne, kada wani ya yaudare su; kama daga ‘yan siyasa, ‘yan jarida, ko kuma ‘yan kasuwa”.

“Mu ba ‘yan siyasa ba ne, aikinmu shi ne kare Kundin Tsarin Mulki. Don haka, ina magana ne ga kowa da kowa da ke da niyyar yaudarar kowane jami’in Sojojin ta hanyar da ba ta dace ba, ”in ji shi.

Shugaban rundunar sojin ya yi wannan jawabi ne a lokacin kaddamar da wani sabon wurin kwana ga jami’an da ke babban ofishin rundunar da ke Kumasi.

An gudanar da aikin ne da nufin inganta rayuwar jami’an soji, wanda ke karkashin kulawar Birgediya Janar Michael Kwadwo Opoku, babban kwamandan runduna ta tsakiya.

Ana sa ran sabon ginin da aka kaddamar zai inganta jin dadin jami’an soji da ke yankin, a daidai lokacin da rundunar ke shirin tallafawa kokarin kasar na gudanar da zabe cikin nasara da lumana a cikin watan Disamba.

A wani labarin kuma, Amurka za ta hana wasu ‘yan ghana biza. Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da Ghana ke shirin gudanar da zaben shugaban kasa a watan Disambar 2024.

Amurka ta sanar da wani tsarin takaita biza ga mutanen da hukumomin Washington ke ganin suna da alhakin haifar da cikas ga tsarin dimokradiyya a Ghana, gabanin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar da za a gudanar a watan Disamba a kasar wacce ke Yammacin Afirka.

“Wannan tsarin takaita biza zai shafi wasu mutanen da ke cin dunduniyar tsarin dimokradiyya ne kawai kuma ba ana nufin za ta shafi al’ummar Ghana ba ko kuma gwamnatin Ghana,” in ji Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a ranar Litinin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GhanaSojojiTsaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yau Za’a Kece Raini Tsakanin Manchester United Da Chelsea A Old Trafford 

Next Post

Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta ‘Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

Related

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
Kasashen Ketare

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

2 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

1 week ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

2 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

3 weeks ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

3 weeks ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

3 weeks ago
Next Post
Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta ‘Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

Ɗaliban Cyprus: Zamfara Ta Samar Wa Ɗalibanta 'Yanci Da Ke Karatu A Gida Da Ƙetare

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.