Babban jami’in diflomasiyyar EU Joao Crabinho da ke matsayin manzon Turai na musamman a Sahel, ya yi gargadin yiwuwar fuskantar sake bazuwar ayyukan ta’addanci a yankin maimakon lafawarsu duk kuwa da kokarin da gwamnatocin yankin ke ikirarin yi.
Kalaman na Crabinho na zuwa bayan fitar alkaluman kungiyar Global Terrorism Inded da ke bayyana yankin na Sahel a matsayin cibiyar ta’addancin duniya sakamakon karuwar tarin kungiyoyin da ke biyayya ga Al-Kaeda da sauran masu ikirarin jihadi musamman a kasashe irin Burkina Faso da Mali da kuma Nijar.
- Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni
- Ziyayar Shugaban Faransa A Kasar Sin Karin Dama Ce Ta Yaukaka Ci Gaban Turai Da Duniya Baki Daya
Jami’in diflomasiyyar na EU yayin jawabinsa gaban wani taron daidaita matsalar ‘yanciranin yankin Sahel ya bayyana cewa kasancewar ‘yan ta’adda basu iya zama a waje daya, suna fantsamuwa ne yankuna tare da daukar sabbin mayaka a duk inda suka yada zango, wannan na nuna yadda barazanarsu ka iya karade kasashen yankin banki daya.
Jami’in ya ce barazanar ‘yan ta’addan bata tsaya ga yankin na Sahel kadai ko kuma nahiyar Afrika ba, babbar barazana ce hatta ga sauran nahiyoyi, ganin yadda ‘yan ta’adda ke ci gaba da yada manufofinsu.
Jami’in ya nanata cewa tsaron Turai na cikin wani yanayi saboda tsanantar ta’addancin a Sahel, yayinda ya yi gargadi kan karuwar dimbin ‘yanciranin da ke kwarara Turai a kowacce rana wanda da ya ce lamari da ke bukatar nazari matuka.
Babban jami’in diflomasiyyar na EU ya ce Turai na bukatar hada karfi da kasashe irin Ghana da Ibory Coast da kuma Mauritania don tunkarar wannan matsala.














