ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnan Ondo: Jam’iyyu Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya – INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Ondo

Gabanin zaben gwamnan Jihar Ondo da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jam’iyyun siyasar da za su fafata a zaben za su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar 8 ga watan Nuwamba a Akure, babban birnin jihar.
Yarjejeniyar zaman lafiya da kwamitin zaman lafiya na kasa (NPC) da INEC suka shirya, wani bangare ne na kokarin ganin an gudanar da zaben cikin lumana.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin wani taro da kungiyoyin farar hula.

  • Kurar Da Ta Biyo Bayan Gurfanar Da Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Yakubu ya kara da cewa INEC za ta gudanar da tantancewar karshe na shirye-shiryenta a mako mai zuwa, wanda zai hada da masu ruwa da tsaki, jami’ai, hukumomin tsaro, da masu samar da sufuri. Ya kuma tabbatar da cewa hukumar ta gano wasu guraren da za a iya ta da zaune tsaye a Jihar Ondo tare da sanar da jami’an tsaro don samar da ingantaccen tsaro da matakan kariya.

ADVERTISEMENT

Dangane da shirin masu kada kuri’a kuwa, Yakubu ya ruwaito cewa daga cikin katinan zabe guda 89,777 da aka raba wa Jihar Ondo, guda 64,273 ne aka amsa, wanda ya nuna an samu kashi 71.6 cikin dari. Ya kara da cewa, nan ba da dadewa ba za a sanya alkaluman tattara bayanai na katin zabe na kowanne daga cikin rumfunan zabe 3,933 a fadin jihar a shafin hukumar INEC, inda za a tabbatar da gaskiya wajen gudanar da sakamakon zaben.

Yakubu ya kuma yi karin haske kan ci gaban da aka samu a harkar zabe da suka hada da tantance masu kada kuri’a, shigar da sakamakon zabe zuwa na’urar INEC ta hanyar duba sakamakon zabe (IReV), da kuma amincewa da masu sa ido da kuma manema labarai.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.