ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnan Ondo: Jam’iyyu Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya – INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Ondo

Gabanin zaben gwamnan Jihar Ondo da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jam’iyyun siyasar da za su fafata a zaben za su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar 8 ga watan Nuwamba a Akure, babban birnin jihar.
Yarjejeniyar zaman lafiya da kwamitin zaman lafiya na kasa (NPC) da INEC suka shirya, wani bangare ne na kokarin ganin an gudanar da zaben cikin lumana.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin wani taro da kungiyoyin farar hula.

  • Kurar Da Ta Biyo Bayan Gurfanar Da Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Yakubu ya kara da cewa INEC za ta gudanar da tantancewar karshe na shirye-shiryenta a mako mai zuwa, wanda zai hada da masu ruwa da tsaki, jami’ai, hukumomin tsaro, da masu samar da sufuri. Ya kuma tabbatar da cewa hukumar ta gano wasu guraren da za a iya ta da zaune tsaye a Jihar Ondo tare da sanar da jami’an tsaro don samar da ingantaccen tsaro da matakan kariya.

ADVERTISEMENT

Dangane da shirin masu kada kuri’a kuwa, Yakubu ya ruwaito cewa daga cikin katinan zabe guda 89,777 da aka raba wa Jihar Ondo, guda 64,273 ne aka amsa, wanda ya nuna an samu kashi 71.6 cikin dari. Ya kara da cewa, nan ba da dadewa ba za a sanya alkaluman tattara bayanai na katin zabe na kowanne daga cikin rumfunan zabe 3,933 a fadin jihar a shafin hukumar INEC, inda za a tabbatar da gaskiya wajen gudanar da sakamakon zaben.

Yakubu ya kuma yi karin haske kan ci gaban da aka samu a harkar zabe da suka hada da tantance masu kada kuri’a, shigar da sakamakon zabe zuwa na’urar INEC ta hanyar duba sakamakon zabe (IReV), da kuma amincewa da masu sa ido da kuma manema labarai.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

LABARAI MASU NASABA

PDP Ba Ta Mutu Ba Duk Da Rikicin Da Ta Ke Fama Da Shi – Anyanwu

PDP Ba Ta Mutu Ba Duk Da Rikicin Da Ta Ke Fama Da Shi – Anyanwu

November 18, 2025
Shugabar Tanzania Ta Bai Wa ’Yarta Da Sirikinta Muƙamin Minista

Shugabar Tanzania Ta Bai Wa ’Yarta Da Sirikinta Muƙamin Minista

November 18, 2025
Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno

Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno

November 18, 2025
Bukatar Samar Da Cikkakken Tsaro Ga Hukumar Zabe

’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

November 18, 2025
Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.