• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan majalisar wakilai biyu daga jihar Kano, wadanda ke wakiltar jam’iyyar NNPP, sun bayyana ficewa daga tafiyar Kwankwasiyya karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

‘Yan majalisar wakilai biyu da suka hada da Aliyu Sani Madakin Gini, mai wakiltar Kano Municipal da Alhassan Rurum (Rano/Kibiya/Bunkure) sun tabbatar da cewa ba za su ci gaba da tafiyar Kwankwasiyya ba, lamarin da ke nuna cewa rikicin jam’iyyar NNPP a Kano ya kara kazancewa a halin yanzu.

  • Tinubu Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Amurka
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Kasa Da Kasa Game Da Tsaffin Al’adun Wayewar Kan Al’umma

Rurum, wanda tsohon shugaban majalisar dokokin Jihar Kano ne ya bayyana ficewarsa daga Kwankwasiyya a wata gajeriyar tattaunawa ta wayar tarho da jaridar Daily Trust.

Duk da dai bai bayar da wasu takamaiman dalilan da ya sa ya yanke wannan shawarar ba kafin karshen wayar, ana ganin ficewar Rurum na da alaka da rikicin da ya barke a baya-bayan nan da gwamnatin Jihar Kano karkashin jam’iyyar NNPP, musamman biyo bayan rusa masarautun biyar da gwamnatin ta yi.

Matakin dai ya shafi Rurum ne kai tsaye, domin yana rike da sarautar gargajiya ta Turakin Rano a cikin masarautar Rano da aka rushe a yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

A nasa bangaren, Madakin Gini wanda shi ne mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai ya fito fili ya nisanta kansa daga Kwankwasiyya yayin da yake jawabi ga al’ummar mazabarsa a Kano ranar Lahadi.
“Daga yau, ni Aliyu Sani Madaki, ba ni da wata alaka da tafiyar Kwankwasiyya.

“Sun kore mu, sun ce ba mu da goyon baya, amma ba ma tsoron mu tsaya mu kadai. Su sani, babu wanda ba zan iya tinkara ba a tafiyar Kwankwasiyya daga sama har kasa, idan akwai bukatar hakan,” in ji shi.

Ya soki kungiyar Kwankwasiyya, wanda aka fi sani da alamar jajayen hula, dangane da yadda take tafiyar da jagorancinta.

Madaki Gini ya ce, “Wannan kungiya ta Kwankwasiyya, idan ya kasance kamar addini ce, to mun biya man biya hakkinmu. Amma sun ce ba mu da amfani, cewa ba mu da goyon bayan al’umma. Ya kamata su gane cewa babu wani a cikin Kwankwasiyya da ba zan iya fuskantarsa ba kai tsaye.”

A wani sako kai tsaye da ya aike wa magoya bayansa, Madakin Gini ya bukace su da su yi watsi da jar hula, inda ya kira hakan alama ce ta mika wuya da ya daina amincewa da ita. “Daga yanzu duk wanda ya dauke ni shugabansa a siyasa, to ya cire jar hula. Mata su cire jajayen mayafi. Mun gama!”
Da yake jawabi kan gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, Madakin Gini ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnan ke fuskantar matsin lamba a cikin tafiyar Kwankwasiyya.

Ya ce, “Sakona ga gwamna a fili yake. Suna kokarin raunata shi. Ina kira a gare shi ya tsaya da kafafuwansa, in ba haka ba, yana iya ruftawa. Ina da basira game da tsare-tsare a kansa.”

Idan dai za a iya tunawa a kwanakin baya ne wata kungiya ta fara wani yunkuri na neman gwamnan ya tsaya da kafafuwansa, ya daina daukar umurni daga wurin uban gidansa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, wanda suka yi zargin cewa shi ke juya gwamnan wurin harkokin yau da kullum na gwamnati.

Haka zalika, rikicin da ke cikin jam’iyyar NNPP mai mulki a Kano na neman kazancewa, inda gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya fara kin daga wayar mai gidansa Rabi’u Musa Kwankwaso, sannan ya ki halartar tarukan da jagoran NNPP na kasa ya shirya.

Da alama dai wannan taken na “Abba tsaya da kafarka” ya fara tasiri a gurin gwamnan bayan da wasu ke ta motsa yadda zai karbe iko da jam’iyyar da kuma Kwankwasiyya daga hannun Kwankwaso.

Wasu majiyoyi sun shaida cewa tuni Abba ya fara amsa kira bayan da aka nusar da shi cewa Kwankwaso ne ke juya gwamnatinsa, inda kusan kashi 90 na makaman da Abba ya yi daga bangaren Kwankwaso ne.

Majiyoyi sun bayyana cewa Abba ba ya jin dadin karfa-karfa da Kwankwaso yake yi masa, inda ya fara nuna alamun bore domin ci gabansa na siyasa da ma Jihar Kano baki daya.

Tun lokacin da aka ga gwamnan a bikin murnar zagayowar haihuwar Kwankwaso, har yanzu ba su sake haduwa ba. Majiyoyi sun bayyana cewa duk tarukan da Kwankwaso ya kira a Kano da Abuja, Abba bai halarta ba.

Majiyoyin sun kkara da cewa har Abuja Kwankwaso ya bi gwamnan, amma Abba bai bari sun hadu ba, kuma har dan aike ya tura masa amma ya ki ganuwa a wajen Kwankwaso.

“Yanzu haka ana shirin hada kai da wasu ‘yan APC da ‘yan kungiyar Abba tsaya da kafarka wajen samo umarnin kotu da zai kori dukka wadannan ciyamomin da aka rantsar, sai dai a bai wa tsagin da Mai Shari’a Simon Amobeda ya tabbatar ana gobe zabe,” in ji majiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPRikicin Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnan Ondo: Jam’iyyu Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya – INEC

Next Post

Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

46 minutes ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

10 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

11 hours ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.