• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ya Bar Baya Da Kura A Wasu Jihohi

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Labarai
0
Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kura ta turnike sakamakon zaben da aka gudanar a kananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna biyo bayan cece-kuce saboda ba a samu kayan zabe da jami’an zabe a mafi yawan wuraren da aka ce an yi zaben.

Sai dai masu kada kuri’a sun fito a wasu cibiyoyin zabe amma ba su sami daman kada kur’ansu ba sakamakon yadda malaman zaben suka iso a makare.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

A rumfar zabe ta Gwamna Uba Sani da ke Kawo Kaduna ta Arewa an samu fitowar masu kada kuri’a da dama, amma akwati daya tilo da aka yi zargin cewa babu takardar sakamakon zaben, lamarin da ya kai ga zanga-zangar da ta kawo cikas ga sakamakon zaben.

A makarantar firamare da gwamnan ya kada kuri’a, akwai rumfunan zabe guda uku, amma akwati zabe guda daya tilo aka samu matsala, lamarin da ya haifar da tashin hankali, inda aka tattaro motocin Hilud sama da 20 dauke da jami’an tsaro zuwa wurin domin kwantar da taroma, wanda mutane suka dage cewa dole ne a samar da takardar sakamako zabe kamar yadda wasu daga cikinsu ke rera wakar “PDP muke so”.

Saboda tashin hankalin da aka yi, gwamnan ya kasa zuwa wurin da za a gudanar da zaben, sai da aka tara jami’an tsaro da yawa a wurin, sannan ya samu damar kada kuri’a bayan karfe 4 na yamma lokacin da ake sa ran kammala zaben.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Wasu rumfunan zabe sun samu kayan zabe ne bayan ya wuce lokacin kada kuri’a.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Edward Masha, ya yi zargin an tabka magudi a zaben.

Masha, yayin da yake jawabi ga ‘yan jarida, ya nuna damuwa game da bacewar muhimman kayan, musamman takardun sakamakon.

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar PDP za ta kalubalanci lamarin a kotu, sannan kuma za ta ci gaba da nema wa mutane adalci. Masha ya bayyana wasu kura-kurai da tashin hankali da aka samu a lokacin zaben.

Masha ya bukaci masoya dimokuradiyya da hukumomin tsaro da su lura da lamarin, inda ya ce, “Jihar Kaduna ba tana cikin rashin lafiya, kuma dimokuradiyya ta tafi. Muna bukatar mu jawo hankalin jama’a tare da neman adalci.”

Shugaban na PDP ya bukaci ‘yan jam’iyyar da magoya bayansa da ka da su karaya. “Za mu ci gaba da fafutukar tabbatar da dimokuradiyya da adalci. Ba za mu yi kasa a gwiwa ba,” in ji shi.

Tun da farko dai, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna (KAD-SIECOM), ta ce jam’iyyar APC ta lashe dukkanin kujerun shugabannin kananan hukumomi 23 da na kansiloli 255.

Da take bayyana sakamakon zaben, shugabar hukumar, Hajara Mohammed, ta ce jam’iyyun siyasa takwas ne suka shiga zaben, inda APC ta lashe kujerun shugabanni kananan hukumomi 23 da kansiloli 255.

Ta kara da cewa jam’iyyar APC mai mulki ta yi nasara a Birnin-Gwari, Chikun, Igabi, Ikara, Jaba, Jema’a, Kachia, Kaduna ta Arewa, da Kaduna ta Kudu.

Sauran kananan hukumomin da jam’iyyar APC ta lashe a cewar shugabar sun hada da Kagarko, Kajuru, Kaura, Kuaru, Kubau, Kudan, Lere, Makarfi, Sabon Gari, Sanga, Soba, Zango-Kataf da Zariya.

A cewar shugabar SEICOM, ADC, APC, APGA, LP, NNPP, PDP, PRP da YPP ne suka gabatar da ‘yan takararsu a zaben.

Sai dai mutane da dama sun nuna rashin gamsuwarsu kan yadda zaben ya gudana, musamma ma jam’iyyun adawa wanda suka bayyana cewa karfa-karfa kawai aka yi amma ba zabe ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomiKuraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

Next Post

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

1 hour ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

3 hours ago
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

7 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

9 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

12 hours ago
Next Post
APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.