• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ya Bar Baya Da Kura A Wasu Jihohi

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kura ta turnike sakamakon zaben da aka gudanar a kananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna biyo bayan cece-kuce saboda ba a samu kayan zabe da jami’an zabe a mafi yawan wuraren da aka ce an yi zaben.

Sai dai masu kada kuri’a sun fito a wasu cibiyoyin zabe amma ba su sami daman kada kur’ansu ba sakamakon yadda malaman zaben suka iso a makare.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

A rumfar zabe ta Gwamna Uba Sani da ke Kawo Kaduna ta Arewa an samu fitowar masu kada kuri’a da dama, amma akwati daya tilo da aka yi zargin cewa babu takardar sakamakon zaben, lamarin da ya kai ga zanga-zangar da ta kawo cikas ga sakamakon zaben.

A makarantar firamare da gwamnan ya kada kuri’a, akwai rumfunan zabe guda uku, amma akwati zabe guda daya tilo aka samu matsala, lamarin da ya haifar da tashin hankali, inda aka tattaro motocin Hilud sama da 20 dauke da jami’an tsaro zuwa wurin domin kwantar da taroma, wanda mutane suka dage cewa dole ne a samar da takardar sakamako zabe kamar yadda wasu daga cikinsu ke rera wakar “PDP muke so”.

Saboda tashin hankalin da aka yi, gwamnan ya kasa zuwa wurin da za a gudanar da zaben, sai da aka tara jami’an tsaro da yawa a wurin, sannan ya samu damar kada kuri’a bayan karfe 4 na yamma lokacin da ake sa ran kammala zaben.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

Wasu rumfunan zabe sun samu kayan zabe ne bayan ya wuce lokacin kada kuri’a.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Edward Masha, ya yi zargin an tabka magudi a zaben.

Masha, yayin da yake jawabi ga ‘yan jarida, ya nuna damuwa game da bacewar muhimman kayan, musamman takardun sakamakon.

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar PDP za ta kalubalanci lamarin a kotu, sannan kuma za ta ci gaba da nema wa mutane adalci. Masha ya bayyana wasu kura-kurai da tashin hankali da aka samu a lokacin zaben.

Masha ya bukaci masoya dimokuradiyya da hukumomin tsaro da su lura da lamarin, inda ya ce, “Jihar Kaduna ba tana cikin rashin lafiya, kuma dimokuradiyya ta tafi. Muna bukatar mu jawo hankalin jama’a tare da neman adalci.”

Shugaban na PDP ya bukaci ‘yan jam’iyyar da magoya bayansa da ka da su karaya. “Za mu ci gaba da fafutukar tabbatar da dimokuradiyya da adalci. Ba za mu yi kasa a gwiwa ba,” in ji shi.

Tun da farko dai, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna (KAD-SIECOM), ta ce jam’iyyar APC ta lashe dukkanin kujerun shugabannin kananan hukumomi 23 da na kansiloli 255.

Da take bayyana sakamakon zaben, shugabar hukumar, Hajara Mohammed, ta ce jam’iyyun siyasa takwas ne suka shiga zaben, inda APC ta lashe kujerun shugabanni kananan hukumomi 23 da kansiloli 255.

Ta kara da cewa jam’iyyar APC mai mulki ta yi nasara a Birnin-Gwari, Chikun, Igabi, Ikara, Jaba, Jema’a, Kachia, Kaduna ta Arewa, da Kaduna ta Kudu.

Sauran kananan hukumomin da jam’iyyar APC ta lashe a cewar shugabar sun hada da Kagarko, Kajuru, Kaura, Kuaru, Kubau, Kudan, Lere, Makarfi, Sabon Gari, Sanga, Soba, Zango-Kataf da Zariya.

A cewar shugabar SEICOM, ADC, APC, APGA, LP, NNPP, PDP, PRP da YPP ne suka gabatar da ‘yan takararsu a zaben.

Sai dai mutane da dama sun nuna rashin gamsuwarsu kan yadda zaben ya gudana, musamma ma jam’iyyun adawa wanda suka bayyana cewa karfa-karfa kawai aka yi amma ba zabe ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomiKuraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

Next Post

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

2 hours ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

2 hours ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

17 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

18 hours ago
Next Post
APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.