ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ya Bar Baya Da Kura A Wasu Jihohi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zaben

Kura ta turnike sakamakon zaben da aka gudanar a kananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna biyo bayan cece-kuce saboda ba a samu kayan zabe da jami’an zabe a mafi yawan wuraren da aka ce an yi zaben.

Sai dai masu kada kuri’a sun fito a wasu cibiyoyin zabe amma ba su sami daman kada kur’ansu ba sakamakon yadda malaman zaben suka iso a makare.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

A rumfar zabe ta Gwamna Uba Sani da ke Kawo Kaduna ta Arewa an samu fitowar masu kada kuri’a da dama, amma akwati daya tilo da aka yi zargin cewa babu takardar sakamakon zaben, lamarin da ya kai ga zanga-zangar da ta kawo cikas ga sakamakon zaben.

ADVERTISEMENT

A makarantar firamare da gwamnan ya kada kuri’a, akwai rumfunan zabe guda uku, amma akwati zabe guda daya tilo aka samu matsala, lamarin da ya haifar da tashin hankali, inda aka tattaro motocin Hilud sama da 20 dauke da jami’an tsaro zuwa wurin domin kwantar da taroma, wanda mutane suka dage cewa dole ne a samar da takardar sakamako zabe kamar yadda wasu daga cikinsu ke rera wakar “PDP muke so”.

Saboda tashin hankalin da aka yi, gwamnan ya kasa zuwa wurin da za a gudanar da zaben, sai da aka tara jami’an tsaro da yawa a wurin, sannan ya samu damar kada kuri’a bayan karfe 4 na yamma lokacin da ake sa ran kammala zaben.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Wasu rumfunan zabe sun samu kayan zabe ne bayan ya wuce lokacin kada kuri’a.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Edward Masha, ya yi zargin an tabka magudi a zaben.

Masha, yayin da yake jawabi ga ‘yan jarida, ya nuna damuwa game da bacewar muhimman kayan, musamman takardun sakamakon.

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar PDP za ta kalubalanci lamarin a kotu, sannan kuma za ta ci gaba da nema wa mutane adalci. Masha ya bayyana wasu kura-kurai da tashin hankali da aka samu a lokacin zaben.

Masha ya bukaci masoya dimokuradiyya da hukumomin tsaro da su lura da lamarin, inda ya ce, “Jihar Kaduna ba tana cikin rashin lafiya, kuma dimokuradiyya ta tafi. Muna bukatar mu jawo hankalin jama’a tare da neman adalci.”

Shugaban na PDP ya bukaci ‘yan jam’iyyar da magoya bayansa da ka da su karaya. “Za mu ci gaba da fafutukar tabbatar da dimokuradiyya da adalci. Ba za mu yi kasa a gwiwa ba,” in ji shi.

Tun da farko dai, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna (KAD-SIECOM), ta ce jam’iyyar APC ta lashe dukkanin kujerun shugabannin kananan hukumomi 23 da na kansiloli 255.

Da take bayyana sakamakon zaben, shugabar hukumar, Hajara Mohammed, ta ce jam’iyyun siyasa takwas ne suka shiga zaben, inda APC ta lashe kujerun shugabanni kananan hukumomi 23 da kansiloli 255.

Ta kara da cewa jam’iyyar APC mai mulki ta yi nasara a Birnin-Gwari, Chikun, Igabi, Ikara, Jaba, Jema’a, Kachia, Kaduna ta Arewa, da Kaduna ta Kudu.

Sauran kananan hukumomin da jam’iyyar APC ta lashe a cewar shugabar sun hada da Kagarko, Kajuru, Kaura, Kuaru, Kubau, Kudan, Lere, Makarfi, Sabon Gari, Sanga, Soba, Zango-Kataf da Zariya.

A cewar shugabar SEICOM, ADC, APC, APGA, LP, NNPP, PDP, PRP da YPP ne suka gabatar da ‘yan takararsu a zaben.

Sai dai mutane da dama sun nuna rashin gamsuwarsu kan yadda zaben ya gudana, musamma ma jam’iyyun adawa wanda suka bayyana cewa karfa-karfa kawai aka yi amma ba zabe ba.

Zaben
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.