ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na’urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

by Muhammad and yahuzajere
2 years ago
Kano

A wani yunƙuri na inganta kula da kiwon lafiya, wani asibitin ƙwararru mai zaman kansa da ake kira ‘Best Choice’ ya ɗauki gaɓarar kula da kiwon lafiyar jarirai tare da ƙaddamar da sashin fasaha don kula da Lafiyar Jarirai da aka tsara don magance ciwon shawara da hana lalacewar kwakwalwar ga jarirai.

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Shugaban Asibitin, Auwal Muhammad Lawal, ya ce na’urar ita ce irinta ta farko wanda kwararrun likitoci ke amfani da ita wajan juyen jini cikin fasaha don inganta sakamakon jiyya ga yara.

  • Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Miyagun Kwayoyi A Kano
  • Tinubu Ya Sake Nada Farfesa Sheshe Shugaban Asibitin Koyarwa Na Aminu Kano

A nasa ɓangaren, Dr Abdulmalik Saminu, ya bayyana cewa na’ura ce mai cike da fasaha da ke ɗaukar nauyin fitowar haske kaso 70% na ban mamaki da ke daidaita buƙatar ƙari ko juyen jini.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa ɓullo da wannan na’ura ta zamani ya nuna wani gagarumin ci gaba ne da Asibitin ‘Best Choice’ ya bullo da shi don kula da kiwon lafiyar jarirai.

Saminu ya ce Sashin Kula da Lafiyar Jarirai na iya yin maganin ciwon shawara yadda yakamata cikin ƙwarewa ba tare da ɗaukar yin doguwar jinya ga iyalai ba, da kuma sauƙin kashe kuɗaɗe.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

“Mun fahimci irin yadda iyaye ke faman shan wahala game da yanayin lafiyar ƙananan yara”

“Saboda haka ne muka mai da hankali kan wannan fasaha don sauƙaƙe nauyin da ke kan iyalai da kuma samar wa yara yanayi mafi kyawu, domin samun rayuwa mai kyau”. In Ji Auwal.

Shugaban Asibitin ya bayyana cewa na’urar ita ce irin ta ta farko a Arewacin Nijeriya, kuma ta uku a fadin Nijeriya, kuma tana ba da cikakkiyar kariya da maganin jiyya ga jarirai.

Dr. Abdulmalik Saminu, babban kwararre likita ne a fannin kiwon lafiya ya bayyana fatansa cewa wannan ci gaban zai ƙara ƙarfafa matsayin asibitin na ‘Best Choice’ a matsayin jagora a fannin kula da kiwon lafiyar ƙananan yara, tare da bai wa iyalai ƙwarin guiwa kan kula da ‘yan uwansu.

Saminu ya godewa mamallakin asibitin bisa namijin ƙoƙarin da ya yi na samar da wannan fasaha ta zamani duk da irin tsadar da take da shi.

Da wannan na’urar ta Kula da Lafiyar Jarirai, iyalai da ‘yan uwa ba sa buƙatar neman tafiya ƙasashen waje don neman magani, kamar yadda asibitin na ‘Best Choice’ ke bayar da tabbas kan haka wajen bayar da kulawa ta musamman a cikin gida.

Kano
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Kano
yahuzajere
+ posts Bio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Next Post
Mutane 9 Sun Rasu, 3 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Titin Kano-Zariya

Mutane 9 Sun Rasu, 3 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Titin Kano-Zariya

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.