• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo, babbar birnin Jihar Osun, ta rushe zabukan kananan hukumomin jihar da hukumar zaben jihar (OSIEC), ta gudanar a kwanakin baya.

Da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Ayo-Nathaniel Emmanuel, ya ayyana zabukan kananan hukumomin da OSIEC ta gudanar a ranar Asabar 15 ga watan Oktoban 2022 a matsayin haramtacce da ke cike da kura-kurai bisa gudanar da shi ba tare da bin dokar zabe ta 2022 ba.

  • Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba
  • Al-Mustapha Ya Yi Tonon Silili Kan Shigo Da Makamai Gabanin Zaben 2023

Sannan, kotun ta umarci wadanda aka ce an zaba da su gaggauta ficewa daga sakatariyar kananan hukumomin da ofis-ofis, yayin da ta umarci a sake gudanar da sabon zaben shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli.

Jam’iyyar PDP ce dai ta garzaya kotun inda take rokon kotun da ta dakatar da OSIEC daga ci gaba da tsare-tsaren zaben.

Kodayake, reshen jam’iyyar PDP ta jihar sun yi lale da murna gami da annashuwa bisa wannan hukuncin, sun ce jam’iyyar ta tsaya Kai da fata wajen tutsu ga kokarin Gwamnatin Gwamna Gboyega Oyetola mai barin gado na gudanar da lamura ba bisa ka’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan hukuncin, mai rikon shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Dakta Akindele Adekunle, ya ce, sama da naira biliyan 1.5 da gwamantin Oyetola ta kashe wajen kan walwa da jin dadin ma’aikatan da suka gudanar da zaben Kananan Hukumomin a matsayin kudaden da aka yi asararsu a banza, kari a kan wasu miliyoyi da aka kashe ba bisa ka’ida ba wajen biyan albashi da alawus-alawus na mutanen da ya kira ‘shugabannin kananan hukumomi na bogi’

“Ai tun da farko mun yi gargadin kar a gudanar da dauki dora (selection) na bogi da sunan zabe. Mun bi dukkanin matakan shari’a wajen ganin an hana OSIEC take tsarin demokradiyya. Shugaban hukumar ma da kansa Lauya ne amma ya amince wajen gudanar da abubuwan da suka saba wa doka.

“Wannan hukuncin na nuni da matakan gyara kura-kuran da aka tafka. Kuma fa da gangan gwamnan da ke shirin barin gado ya aikata hakan. Za mu cigaba da bin dukkanin matakan shari’a wajen kare hakkokin al’umman jihar”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomiKotuOsunRushe Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba

Next Post

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

2 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

8 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

9 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

21 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

1 day ago
Next Post
Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.