• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo, babbar birnin Jihar Osun, ta rushe zabukan kananan hukumomin jihar da hukumar zaben jihar (OSIEC), ta gudanar a kwanakin baya.

Da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Ayo-Nathaniel Emmanuel, ya ayyana zabukan kananan hukumomin da OSIEC ta gudanar a ranar Asabar 15 ga watan Oktoban 2022 a matsayin haramtacce da ke cike da kura-kurai bisa gudanar da shi ba tare da bin dokar zabe ta 2022 ba.

  • Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba
  • Al-Mustapha Ya Yi Tonon Silili Kan Shigo Da Makamai Gabanin Zaben 2023

Sannan, kotun ta umarci wadanda aka ce an zaba da su gaggauta ficewa daga sakatariyar kananan hukumomin da ofis-ofis, yayin da ta umarci a sake gudanar da sabon zaben shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli.

Jam’iyyar PDP ce dai ta garzaya kotun inda take rokon kotun da ta dakatar da OSIEC daga ci gaba da tsare-tsaren zaben.

Kodayake, reshen jam’iyyar PDP ta jihar sun yi lale da murna gami da annashuwa bisa wannan hukuncin, sun ce jam’iyyar ta tsaya Kai da fata wajen tutsu ga kokarin Gwamnatin Gwamna Gboyega Oyetola mai barin gado na gudanar da lamura ba bisa ka’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan hukuncin, mai rikon shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Dakta Akindele Adekunle, ya ce, sama da naira biliyan 1.5 da gwamantin Oyetola ta kashe wajen kan walwa da jin dadin ma’aikatan da suka gudanar da zaben Kananan Hukumomin a matsayin kudaden da aka yi asararsu a banza, kari a kan wasu miliyoyi da aka kashe ba bisa ka’ida ba wajen biyan albashi da alawus-alawus na mutanen da ya kira ‘shugabannin kananan hukumomi na bogi’

“Ai tun da farko mun yi gargadin kar a gudanar da dauki dora (selection) na bogi da sunan zabe. Mun bi dukkanin matakan shari’a wajen ganin an hana OSIEC take tsarin demokradiyya. Shugaban hukumar ma da kansa Lauya ne amma ya amince wajen gudanar da abubuwan da suka saba wa doka.

“Wannan hukuncin na nuni da matakan gyara kura-kuran da aka tafka. Kuma fa da gangan gwamnan da ke shirin barin gado ya aikata hakan. Za mu cigaba da bin dukkanin matakan shari’a wajen kare hakkokin al’umman jihar”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomiKotuOsunRushe Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba

Next Post

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Related

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

2 hours ago
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

7 hours ago
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga KuÉ—aÉ—e – Datti
Manyan Labarai

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga KuÉ—aÉ—e – Datti

12 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu
Manyan Labarai

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

13 hours ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya GargaÉ—i Magoya Bayan Wike A PDP

17 hours ago
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya
Manyan Labarai

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

1 day ago
Next Post
Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.