ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Osun

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo, babbar birnin Jihar Osun, ta rushe zabukan kananan hukumomin jihar da hukumar zaben jihar (OSIEC), ta gudanar a kwanakin baya.

Da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Ayo-Nathaniel Emmanuel, ya ayyana zabukan kananan hukumomin da OSIEC ta gudanar a ranar Asabar 15 ga watan Oktoban 2022 a matsayin haramtacce da ke cike da kura-kurai bisa gudanar da shi ba tare da bin dokar zabe ta 2022 ba.

  • Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba
  • Al-Mustapha Ya Yi Tonon Silili Kan Shigo Da Makamai Gabanin Zaben 2023

Sannan, kotun ta umarci wadanda aka ce an zaba da su gaggauta ficewa daga sakatariyar kananan hukumomin da ofis-ofis, yayin da ta umarci a sake gudanar da sabon zaben shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar PDP ce dai ta garzaya kotun inda take rokon kotun da ta dakatar da OSIEC daga ci gaba da tsare-tsaren zaben.

Kodayake, reshen jam’iyyar PDP ta jihar sun yi lale da murna gami da annashuwa bisa wannan hukuncin, sun ce jam’iyyar ta tsaya Kai da fata wajen tutsu ga kokarin Gwamnatin Gwamna Gboyega Oyetola mai barin gado na gudanar da lamura ba bisa ka’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan hukuncin, mai rikon shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Dakta Akindele Adekunle, ya ce, sama da naira biliyan 1.5 da gwamantin Oyetola ta kashe wajen kan walwa da jin dadin ma’aikatan da suka gudanar da zaben Kananan Hukumomin a matsayin kudaden da aka yi asararsu a banza, kari a kan wasu miliyoyi da aka kashe ba bisa ka’ida ba wajen biyan albashi da alawus-alawus na mutanen da ya kira ‘shugabannin kananan hukumomi na bogi’

“Ai tun da farko mun yi gargadin kar a gudanar da dauki dora (selection) na bogi da sunan zabe. Mun bi dukkanin matakan shari’a wajen ganin an hana OSIEC take tsarin demokradiyya. Shugaban hukumar ma da kansa Lauya ne amma ya amince wajen gudanar da abubuwan da suka saba wa doka.

“Wannan hukuncin na nuni da matakan gyara kura-kuran da aka tafka. Kuma fa da gangan gwamnan da ke shirin barin gado ya aikata hakan. Za mu cigaba da bin dukkanin matakan shari’a wajen kare hakkokin al’umman jihar”.

Osun
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.