• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben Kananan Hukumomin Osun Haramtacce Ne – Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo, babbar birnin Jihar Osun, ta rushe zabukan kananan hukumomin jihar da hukumar zaben jihar (OSIEC), ta gudanar a kwanakin baya.

Da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Ayo-Nathaniel Emmanuel, ya ayyana zabukan kananan hukumomin da OSIEC ta gudanar a ranar Asabar 15 ga watan Oktoban 2022 a matsayin haramtacce da ke cike da kura-kurai bisa gudanar da shi ba tare da bin dokar zabe ta 2022 ba.

  • Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba
  • Al-Mustapha Ya Yi Tonon Silili Kan Shigo Da Makamai Gabanin Zaben 2023

Sannan, kotun ta umarci wadanda aka ce an zaba da su gaggauta ficewa daga sakatariyar kananan hukumomin da ofis-ofis, yayin da ta umarci a sake gudanar da sabon zaben shugabannin kananan hukumomi da Kansiloli.

Jam’iyyar PDP ce dai ta garzaya kotun inda take rokon kotun da ta dakatar da OSIEC daga ci gaba da tsare-tsaren zaben.

Kodayake, reshen jam’iyyar PDP ta jihar sun yi lale da murna gami da annashuwa bisa wannan hukuncin, sun ce jam’iyyar ta tsaya Kai da fata wajen tutsu ga kokarin Gwamnatin Gwamna Gboyega Oyetola mai barin gado na gudanar da lamura ba bisa ka’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nada ÆŠan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan hukuncin, mai rikon shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Dakta Akindele Adekunle, ya ce, sama da naira biliyan 1.5 da gwamantin Oyetola ta kashe wajen kan walwa da jin dadin ma’aikatan da suka gudanar da zaben Kananan Hukumomin a matsayin kudaden da aka yi asararsu a banza, kari a kan wasu miliyoyi da aka kashe ba bisa ka’ida ba wajen biyan albashi da alawus-alawus na mutanen da ya kira ‘shugabannin kananan hukumomi na bogi’

“Ai tun da farko mun yi gargadin kar a gudanar da dauki dora (selection) na bogi da sunan zabe. Mun bi dukkanin matakan shari’a wajen ganin an hana OSIEC take tsarin demokradiyya. Shugaban hukumar ma da kansa Lauya ne amma ya amince wajen gudanar da abubuwan da suka saba wa doka.

“Wannan hukuncin na nuni da matakan gyara kura-kuran da aka tafka. Kuma fa da gangan gwamnan da ke shirin barin gado ya aikata hakan. Za mu cigaba da bin dukkanin matakan shari’a wajen kare hakkokin al’umman jihar”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomiKotuOsunRushe Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taiwan Bangare Ne Da Ba Za A Iya Raba Shi Da Kasar Sin Ba

Next Post

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada ÆŠan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

12 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

17 hours ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 day ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

1 day ago
Next Post
Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

Nijeriya Na Iya Fuskantar Karancin Abinci A 2023 –IMF

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.