• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hanyar da kasar Sin ke bi wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya ta sha bamban da ta Amurka, inda a lokuta da dama Sin ke jaddada amfani da diflomasiyya, da hadin gwiwar tattalin arziki, da kuma manufofin guje wa katsalandan ga sauran kasashe.

 

Yunkurin Sin a kan wanzar da zaman lafiya ya kasance sananne ne ta hanyar karfafa hadin gwiwar tattalin arziki maimakon daukar matakin soji wadda kan haka ne ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRI da ta fi mayar da hankali kan bunkasa ababen more rayuwa da hadin gwiwar kasuwanci, da samar da kwanciyar hankali ta hanyar dogaro da tattalin arziki maimakon amfani da karfin soja. Sabanin haka, a tarihi Amurka ta dogara ce da kawancen soji da yin katsalandan wadda a lokuta da dama ke haifar da tsawaita rikice-rikice maimakon magancewa.

  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Shawarar BRI ta kasance babban misali na diflomasiyyar kasar Sin a kan raya tattalin arzikin duniya ta hanyar ayyukan samar da ababen more rayuwa a fadin Asiya, Afirka, da Turai da Latin Amurka. Kasar Sin ta karfafa dogaro da juna kan tattalin arziki, tare da rage yiwuwar afkuwar rikice-rikice. Kasashen da ke cin gajiyar zuba jari na BRI galibi suna ba da fifikon kasuwanci da hadin gwiwa fiye da tashe-tashen hankula na siyasa.

Kasar Sin na bin manufar rashin tsoma baki a harkokin cikin gidan wasu kasashe, ka’idar da ta samo asali daga akidarta ta diflomasiyya, inda ta sha bamban da Amurka, wacce ta tsunduma cikin ayyukan tumbuke gwamnatocin kasashe da kuma daukar matakan soja a yankuna daban-daban. Matsayin kasar Sin na son zaman lafiya ya ba ta damar ci gaba da kyautata dangantaka da gwamnatoci daban-daban ba tare da kyamar tsarin siyasar kasashensu ba.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin ta ci gaba da yin tsayin daka kan matsayinta na guje wa yin katsalandan musamman a Afirka. Ba kamar kasashen yammacin duniya da suka tsunduma cikin harkokin soji da makamai ba, kasar ta mai da hankali kan hadin gwiwar tattalin arziki, kamar zuba jari mai yawa a kasashen Afirka da dama ba tare da gindaya sharuddan siyasa ba. Wannan tsarin ya taimaka wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin.

Kazalika, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da sulhunta rikici a yankin Asiya, inda ta samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin da ke rikici da juna maimakon samar da mafita ta hanyar karfin soja. Sulhunta tsakanin Saudiya da Iran a shekarar 2023, tare da daidaita harkokin diflomasiyya tsakanin kasashen biyu babban misali ne. Wannan nasarar ta nuna hikimar da kasar Sin ke da ita ta sasanta rikice-rikice masu sarkakiya a matakin yanki ba tare da tilastawa ko kuma matsin lamba ta fuskar soja ba. Sabanin Amurka wacce ake suka bisa dama lissafi da kara zaman dar-dar, musamman a yankin Asiya da tekun Pasifik, ta hanyar kawancen soji da sayar da makamai.

Kasar Sin da gaske take yi kan batun zaman lafiya a duniya, domin yayin da Amurka kullum ke tunanin fadada sansanoninta na soji, ita kuwa ta fi mayar da hankali ne wajen sabuntawa da karfafa rundunonin sojinta don kiyaye tsaron kanta da ikon mallakar yankunanta. Ba kamar Amurka ba, wacce ke daukar dawainiyar sansanonin soji birjik a duniya da a ko yaushe ake zarginsu da haddasa husuma a yankuna.

Ba wai kawai a doron kasa ba, hatta ci gaban da ake samu na bincike a sararin samaniya Amurka ta mayar da shi ta fuskar soji, duk kuwa da gargadin da ake ta yi cewa hakan zai haifar da gasar makamai da kara tabarbarewar tsaro a duniya. A nata bangaren, kasar Sin jaddada hadin gwiwar kimiyya ta yi, kamar samar da tashar binciken sararin samaniya ta Tiangong, wadda ke maraba da hadin gwiwar kasa da kasa. Wannan ma ya bambanta da kafa rundunar sararin samaniyar da Amurka ta yi, wadda ke nuni da mayar da lamarin ta fuskar soji.

Akidar Sin ta yin hadin gwiwar tattalin arziki, da sulhuntawa a fannin diflomasiyya, sun ba ta damar ci gaba da yin suna a matsayin mai tabbatar da zaman lafiya a harkokin duniya. Yayin da Amurka kuma ke ci gaba da yin tasiri ta hanyar kawancen soja da yin katsalandan ga sauran kasashe. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Next Post

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

17 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

18 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

19 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

20 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

22 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

LABARAI MASU NASABA

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.