ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Amurka

Hanyar da kasar Sin ke bi wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya ta sha bamban da ta Amurka, inda a lokuta da dama Sin ke jaddada amfani da diflomasiyya, da hadin gwiwar tattalin arziki, da kuma manufofin guje wa katsalandan ga sauran kasashe.

 

Yunkurin Sin a kan wanzar da zaman lafiya ya kasance sananne ne ta hanyar karfafa hadin gwiwar tattalin arziki maimakon daukar matakin soji wadda kan haka ne ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRI da ta fi mayar da hankali kan bunkasa ababen more rayuwa da hadin gwiwar kasuwanci, da samar da kwanciyar hankali ta hanyar dogaro da tattalin arziki maimakon amfani da karfin soja. Sabanin haka, a tarihi Amurka ta dogara ce da kawancen soji da yin katsalandan wadda a lokuta da dama ke haifar da tsawaita rikice-rikice maimakon magancewa.

ADVERTISEMENT
  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Shawarar BRI ta kasance babban misali na diflomasiyyar kasar Sin a kan raya tattalin arzikin duniya ta hanyar ayyukan samar da ababen more rayuwa a fadin Asiya, Afirka, da Turai da Latin Amurka. Kasar Sin ta karfafa dogaro da juna kan tattalin arziki, tare da rage yiwuwar afkuwar rikice-rikice. Kasashen da ke cin gajiyar zuba jari na BRI galibi suna ba da fifikon kasuwanci da hadin gwiwa fiye da tashe-tashen hankula na siyasa.

Kasar Sin na bin manufar rashin tsoma baki a harkokin cikin gidan wasu kasashe, ka’idar da ta samo asali daga akidarta ta diflomasiyya, inda ta sha bamban da Amurka, wacce ta tsunduma cikin ayyukan tumbuke gwamnatocin kasashe da kuma daukar matakan soja a yankuna daban-daban. Matsayin kasar Sin na son zaman lafiya ya ba ta damar ci gaba da kyautata dangantaka da gwamnatoci daban-daban ba tare da kyamar tsarin siyasar kasashensu ba.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kasar Sin ta ci gaba da yin tsayin daka kan matsayinta na guje wa yin katsalandan musamman a Afirka. Ba kamar kasashen yammacin duniya da suka tsunduma cikin harkokin soji da makamai ba, kasar ta mai da hankali kan hadin gwiwar tattalin arziki, kamar zuba jari mai yawa a kasashen Afirka da dama ba tare da gindaya sharuddan siyasa ba. Wannan tsarin ya taimaka wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin.

Kazalika, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da sulhunta rikici a yankin Asiya, inda ta samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin da ke rikici da juna maimakon samar da mafita ta hanyar karfin soja. Sulhunta tsakanin Saudiya da Iran a shekarar 2023, tare da daidaita harkokin diflomasiyya tsakanin kasashen biyu babban misali ne. Wannan nasarar ta nuna hikimar da kasar Sin ke da ita ta sasanta rikice-rikice masu sarkakiya a matakin yanki ba tare da tilastawa ko kuma matsin lamba ta fuskar soja ba. Sabanin Amurka wacce ake suka bisa dama lissafi da kara zaman dar-dar, musamman a yankin Asiya da tekun Pasifik, ta hanyar kawancen soji da sayar da makamai.

Kasar Sin da gaske take yi kan batun zaman lafiya a duniya, domin yayin da Amurka kullum ke tunanin fadada sansanoninta na soji, ita kuwa ta fi mayar da hankali ne wajen sabuntawa da karfafa rundunonin sojinta don kiyaye tsaron kanta da ikon mallakar yankunanta. Ba kamar Amurka ba, wacce ke daukar dawainiyar sansanonin soji birjik a duniya da a ko yaushe ake zarginsu da haddasa husuma a yankuna.

Ba wai kawai a doron kasa ba, hatta ci gaban da ake samu na bincike a sararin samaniya Amurka ta mayar da shi ta fuskar soji, duk kuwa da gargadin da ake ta yi cewa hakan zai haifar da gasar makamai da kara tabarbarewar tsaro a duniya. A nata bangaren, kasar Sin jaddada hadin gwiwar kimiyya ta yi, kamar samar da tashar binciken sararin samaniya ta Tiangong, wadda ke maraba da hadin gwiwar kasa da kasa. Wannan ma ya bambanta da kafa rundunar sararin samaniyar da Amurka ta yi, wadda ke nuni da mayar da lamarin ta fuskar soji.

Akidar Sin ta yin hadin gwiwar tattalin arziki, da sulhuntawa a fannin diflomasiyya, sun ba ta damar ci gaba da yin suna a matsayin mai tabbatar da zaman lafiya a harkokin duniya. Yayin da Amurka kuma ke ci gaba da yin tasiri ta hanyar kawancen soja da yin katsalandan ga sauran kasashe. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?
  • Sulaiman
    ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
  • Sulaiman
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Sulaiman
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
Daga Birnin Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
Daga Birnin Sin

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Next Post
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026
Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.