• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), Antonio Gutteres ya dauki nauyin samar da wani tsari mai suna “Karfafa Zaman Lafiya a Kananan Hukumomi da Jihohin Katsina da Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya”.

Yankin Arewa maso Yamma, musamman Jihohin Kaduna da Katsina, na fama da matsalolin da suka shafi rikicin manoma da makiya, da rikicin kabilanci da ta’addanci da sauransu.

Domin samun nasarar tsarin, an gudanar da wani taro na musamman a ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, ranar Alhamis, don neman goyon baya da tabbatar da zaman lafiya da yaki da ‘yan bindiga musamman a Jihohin Kaduna da Katsina.

  • Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli
  • Maulidin Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Reshen Sakkwato Ya Yi Armashi

Babban Jami’in gudanarwa na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya, Mista Matthias Schmale, a sanarwar da ya fitar ga manema labarai, ya ce, babban dalilin da ya sa aka kafa Majalisar Dinkin Duniya shi ne samar da zaman lafiya tsakanin kasashe. Domin haka, ya zama wajibi majalisar ta tabbatar da cewa an samu zaman lafiya a duniya tare da kai ɗauki ga musamman Jihohin Katsina da Kaduna bisa yadda suke buƙatar taimako.

zaman lafiya
Yayin gudanar da taron

A nashi ɓangaren, Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya bayyana cewa: “A halin yanzu kananan hukumomi 8 da ke maƙotaka da Nijar na fuskantar hare-haren ‘yan bindiga. Bugu da kari, akwai kananan hukumomi sama da 14 baya ga wadannan 8, da a kowace rana ina samun rahotanni kan hare-haren da ake kai wa kauyuka a cikinsu.”

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Gwamnan ya kara da cewa: “An dauki jami’an tsaro tare da tura su kauyukan domin dakile hare-haren da ake kaiwa a yankunan”.

Har ila yau, Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani wanda mai ba shi shawara na musamman kan samar da zaman lafiya, Atiku Sanke, ya wakilta, ya ba da tabbacin goyon baya wajen ganin an samar da ayyukan da za su tabbatar da zaman lafiya a jihar.

zaman lafiya
Mista Matthias Schmale tare da Gwamna Radda na Katsina

Babbar manufar shirin mai lakabin PBF I4P, ita ce karfafa wa Gwamnatin Jihohin Kaduna da Katsina kwarin gwiwa don samar da hadin kai da hanyoyin zaman lafiya da rigakafin matsalolin da rikice-rikice suke haifawarwa.

Hukumomin da suka hadu wurin samar da wannan sabon tsari na zaman lafiya sun hada da: UNDP, Sashen Kula da Mata na MDD (UN Women), da IOM tare da tallafin Cibiyar OHCHR, domin bayar da gudunmawa ga mutunta hakkin Da’adam.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKatsinaMDDTaroTsaroZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekaru Goma Masu Albarka: Yadda Shawarar Ziri Ɗaya Da Hanya Ɗaya Ta Yi Kyakkyawar Tasiri Ga Kasashen Afirka

Next Post

Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

Wani Matashi Ya Mayar Da Kusan Miliyan 100 Da Aka Turo Asusunsa Na Banki Bisa Kuskure

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.