• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 14 ga watan Yuni, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas a nan birnin Beijing. Sun sanar da kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Falasdinu.

Shugaba Xi ya gabatar da shawarwari mai kunshe da abubuwa uku na warware batun Falasdinu. Ya bayyana cewa babbar hanyar warware batun Falasdinawa ita ce kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta wacce ke da cikakken ikon mallakar kai a bisa yarjejeniyar kan iyakoki ta shekarar 1967 da kuma gabashin Kudus a matsayin babban birninta.

  • Shugaba Xi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kamata a biya bukatun tattalin arziki da rayuwar Falasdinawa, sannan kasashen duniya su kara kaimi wajen taimakon raya kasa da taimakon jin kai ga Falasdinu. Kuma a karshe, yana da muhimmanci a kiyaye hanyar da ta dace na tattaunawar da za ta kai ga zaman lafiya.

Hanyar da kasar Sin ke bi na samun zaman lafiya ta samo asali ne daga tsohuwar hikimar kasar Sin, kamar yadda yake bayyane a cikin wadannan kalamai: “Bai kamata masu karfi da masu kudi su rika zaluntar marasa karfi da matalauta ba”, kuma “duk kasar da ke takama da karfin yaki, duk girmanta, daga karshe za ta durkushe.” Wadannan kalmomi masu zurfi suna misalta kimar kasar Sin yayin da take tafiyar da tsarin kasa da kasa mai sarkakiya da rashin kwanciyar hankali, tare da neman hanyar zaman lafiya da ci gaba, ta hanyar tattaunawa da mutunta ’yancin juna ba tare da katsalandan ko shisshigi ba.

Abin da ke tattare da irin wannan yunkurin na kasar Sin shi ne wasu suka mayar da batun tattaunawa game da babbar hamayya tsakanin manyan tattalin arzikin duniya guda biyu. A wannan yanayi, an mayar da hankali kan Sin da Amurka a Gabas ta Tsakiya, da tabarbarewar alakar da ke tsakaninsu. Sanin kowa ne cewa Amurka da Isra’ila sun kulla alaka mai karfi ta tsaro, da tattalin arziki da siyasa.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

Kuma idan aka yi la’akari da yanayin siyasa mai sarkakiya a yankin, yin nazari game da dangantakar abota tsakanin kasar Sin da Falasdinu, wani zai dauka kasar Sin na kalubalantar Amurka ne.

Kasar Sin ba ta da sha’awar kalubalantar Amurka a Gabas ta Tsakiya ko kuma a ko’ina. Tasirin da Amurka ke da shi a yankin na kara raguwa saboda tsarin siyasarta da bukatunta. Babu wanda za a zarga da sanyaya dangantakar Amurka da yankin Gabas ta Tsakiya face zabin da Amurka ta yiwa kanta.

Akidar Confucius ta kayyade cewa “ya kamata mutum ya nemi jituwa a cikin bambance-bambance kuma kada ya yi wa wasu abin da ba zai so a masa ba.” Burin kasar Sin shi ne ta samar da daidaito a wannan duniyar da ke cike da bambance-bambance. Kuma tana taimaka wa kasashen Gabas ta Tsakiya da hakan. (Yahaya Babs)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Next Post

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Related

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

36 minutes ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

2 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

4 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

4 hours ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

20 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

22 hours ago
Next Post
Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.