• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 14 ga watan Yuni, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas a nan birnin Beijing. Sun sanar da kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Falasdinu.

Shugaba Xi ya gabatar da shawarwari mai kunshe da abubuwa uku na warware batun Falasdinu. Ya bayyana cewa babbar hanyar warware batun Falasdinawa ita ce kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta wacce ke da cikakken ikon mallakar kai a bisa yarjejeniyar kan iyakoki ta shekarar 1967 da kuma gabashin Kudus a matsayin babban birninta.

  • Shugaba Xi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kamata a biya bukatun tattalin arziki da rayuwar Falasdinawa, sannan kasashen duniya su kara kaimi wajen taimakon raya kasa da taimakon jin kai ga Falasdinu. Kuma a karshe, yana da muhimmanci a kiyaye hanyar da ta dace na tattaunawar da za ta kai ga zaman lafiya.

Hanyar da kasar Sin ke bi na samun zaman lafiya ta samo asali ne daga tsohuwar hikimar kasar Sin, kamar yadda yake bayyane a cikin wadannan kalamai: “Bai kamata masu karfi da masu kudi su rika zaluntar marasa karfi da matalauta ba”, kuma “duk kasar da ke takama da karfin yaki, duk girmanta, daga karshe za ta durkushe.” Wadannan kalmomi masu zurfi suna misalta kimar kasar Sin yayin da take tafiyar da tsarin kasa da kasa mai sarkakiya da rashin kwanciyar hankali, tare da neman hanyar zaman lafiya da ci gaba, ta hanyar tattaunawa da mutunta ’yancin juna ba tare da katsalandan ko shisshigi ba.

Abin da ke tattare da irin wannan yunkurin na kasar Sin shi ne wasu suka mayar da batun tattaunawa game da babbar hamayya tsakanin manyan tattalin arzikin duniya guda biyu. A wannan yanayi, an mayar da hankali kan Sin da Amurka a Gabas ta Tsakiya, da tabarbarewar alakar da ke tsakaninsu. Sanin kowa ne cewa Amurka da Isra’ila sun kulla alaka mai karfi ta tsaro, da tattalin arziki da siyasa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Kuma idan aka yi la’akari da yanayin siyasa mai sarkakiya a yankin, yin nazari game da dangantakar abota tsakanin kasar Sin da Falasdinu, wani zai dauka kasar Sin na kalubalantar Amurka ne.

Kasar Sin ba ta da sha’awar kalubalantar Amurka a Gabas ta Tsakiya ko kuma a ko’ina. Tasirin da Amurka ke da shi a yankin na kara raguwa saboda tsarin siyasarta da bukatunta. Babu wanda za a zarga da sanyaya dangantakar Amurka da yankin Gabas ta Tsakiya face zabin da Amurka ta yiwa kanta.

Akidar Confucius ta kayyade cewa “ya kamata mutum ya nemi jituwa a cikin bambance-bambance kuma kada ya yi wa wasu abin da ba zai so a masa ba.” Burin kasar Sin shi ne ta samar da daidaito a wannan duniyar da ke cike da bambance-bambance. Kuma tana taimaka wa kasashen Gabas ta Tsakiya da hakan. (Yahaya Babs)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Next Post

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Related

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

18 minutes ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

2 hours ago
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

23 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

1 day ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

1 day ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

2 days ago
Next Post
Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.