• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara 2023: An Ƙaryata Jita-jitar Janyewar Takarar Dauda Lawal

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Zamfara 2023: An Ƙaryata Jita-jitar Janyewar Takarar Dauda Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na Dr. Dauda Lawal ya ƙaryata jita-jitar da ake yawo da ita na cewa yana shirin ficewa daga jam’iyyar PDP ya koma APC.

Dr. Dauda Lawal shi ne ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP.

 

  • Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa

A wata takardar sanarwar manema labarai da ofishin yaɗa labaran na Dauda Lawal ya fitar yau Asabar a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara ya ambaci wannan labari da shiryayyen ƙarya domin a ɓata sunan Dauda Lawal ɗin.

Ofishin ya ce, ba gaskiya ba ne batun cewa Dauda Lawal ya yi wata tattauna ta sirri da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Sani Yarima.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna kira ga dukkanin magoya bayan Gamjin Gusau, Dr. Dauda Lawal, ‘ya’yan jam’iyyar PDP da ma al’ummar Jihar Zamfara gabaɗaya da su yi watsi da wata jita-jita da ‘yan adawa suke yawo da ita.

“Jita-jitar tasu ta fi kama da wasan yara, saboda suna yawo da ƙaryar wai ɗan takarar Gwamna mai farin jini a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dauda Lawal zai koma APC.

“Wannan lamari bai bamu mamaki ba, saboda mun san jam’iyya mai mulki ba ta da wani abin arziki da za ta iya yin farfaganda da shi, sai dai su dogara da ƙarairayi da sharri don ganin sun dushe hasken Gamjin Gusau.

“Tun bayan da Dauda Lawal ya ayyana aniyarsa ta yin takara suka shiga cikin ruɗani da fargaba. Bayan da ya lashe zaɓen fidda gwanin PDP na Jihar Zamfara, sai hankulansu suka tashi, suka shiga neman hanyoyin yaɗa sharri.

“Ai abu ne ma da hankali ba zai ɗauka ba, a ce mutumin da aka zaɓa a matsayin ɗan takarar gwamna a wata jam’iyya daban ya ajiye takara ya sauya sheƙa. Wannan irin farfaganda ko ƙananan yara ba za su yarda da ita ba. Ko ba komi wannan alamu ne na nasara, cewa jam’iyya mai mulki ta fahimci lokaci ya ƙure mata, kuma tauraron Dauda Lawal ne ke haskawa yanzu a Zamfara.

 

  • https://leadership.ng/12-quick-facts-about-zamfara-pdp-candidate-dr-dauda-lawal/

“Muna yin amfani da wannan dama wurin sanar da al’umma cewa, duk wata sanarwa da ba ta fito kaitsaye daga wurin ɗan takarar gwamna, Dr. Dauda Lawal ko ofishin yaɗa labaransa ba, a yi watsi da ita.” Inji ofishin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amfanin Manhajar XENDER A Wayoyin Hannu

Next Post

Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

22 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

1 day ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

6 days ago
Next Post
Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.