Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya ja kunnen masu daukar doka a hannunsu da wadan da suka mallaki makamai ta haramtacciyar hanya domin samun riba don su haddasa rashin tsaro a kasar nan za su fuskaci Hukunci kamar yadda dokar kasa ta tanada.
Ya bayyana hakan ranar Alhamis a garin Wudil da ke a jihar Kano yayin bikin yayen dailiban makarantar horas da ‘yan sanda.
- ‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno
- ‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade
Buhari ya ce, gwamnatinsa zata ci gaba da tabbatar da yakar aikata manyan laifuka a fading kasar nan, shugaban ya umarci ‘yan sandan da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu don ganin an tabbatar da doka da Oda.
Buhari ya ce akwai bukatar a samar da na’urar zamani da za ta taimaka wajen dakile ayyukan masu yin kutse a kafar yanar gizo.
Shugaban ya kuma bayyana cewa, yankunan Arewa ta tsakiya da kuma a Arewa ta Yamma sun yi nasara wajen rage rikice-rikice da rikicin manoma da makiyaya da satar shanu da kuma yin garkuwa da mutane.
Ya ce, kai hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram da aikata ayyukan ta’addancin da ‘yan kungiyar IPOB ke yi a wasu sassan Nijeriya da ci gaba da zama barazana ga kasar nan.
Ya ce, gwamnati ta samu nasarar rage ayyukan na su ganin cewa al’amura sun dawo dai dai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp