• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga durkushewa.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake jawabi a taron yakin neman zabensa a Birnin Kebbi na Jihar Kebbi.

  • Emmanuel Bwacha Ya Lashe Zaben Fidda Gwanin APC A Taraba
  • Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

Ya ce, sana’ar kifi a Jihar Kebbi za ta hade da Legas ta yadda zai bunkasa tattalin arzikin jihar tare da samar da karin guraben ayyukan yi ga dimbin matasan jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zai warware matsalar rashin tsaro da karancin mai a jihar.

Dan takarar, ya nuna jin dadinsa kan yadda dimbin magoya baya suka tarbe shi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ya jinjina wa Gwamna Jihar, Atiku Bagudu da shugabannin jam’iyyar APC na jihar da kuma duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin samun nasarar yakin neman zabensa a jihar.

A nasa jawabin, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya bayyana dimbin jama’ar da suka hallara a wurin taron a matsayin shaida ne na kyakkyawan shugabancin Bagudu a jihar.

A cewarsa, “Mun gamsu da fitowar da muka gani a nan filin wasa na Haliru Audu domin yakin neman zaben shugaban kasa. Wannan shaida ce cewar Jihar Kebbi gidan APC ne. Muna godiya ga jama’a da gwamnatin jihar bisa kokarin da suke yi na ganin taron yakin neman zaben shugaban kasa a Birnin Kebbi ya zama kasance cikin nasara.

“Ina kira gare ku, a yayin da kuke taron gangamin nuna goyon baya ga dan takararmu na shugaban kasa a yau da sauran ‘yan takara, da ku sake fitowa ranar 25 ga watan Fabrairu tare da katin zabenku ku zabi dukkan ‘yan takarar APC, domin Asiwaju Bola Ahmed ya samu nasara,” in ji shi.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, a jawabinsa ya ce, dandazon jama’ar da suka fito wajen taron wata alama ce cewa APC za ta lashe zabe a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma yi godiya da goyon bayan da kowa ya ba shi “Ina yi wa dan takarar shugaban kasa da mukarrabansa fatan komawa Abuja lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtiku BaguduJihar KebbiTinubuYakin Neman Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Gaggauta Tura Ma’aikatan Ceto Zuwa Turkiye Da Syria Da Girgizar Kasa Ta Aukawa

Next Post

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

2 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

4 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

5 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

9 hours ago
Next Post
Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.