• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Iya Kera Jirgin Da Zai Yi Shawagi A Ko’ina Cikin Duniya – Dalibin Nnewi

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Nnewi

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Nnewi a jihar Anambra ta sake cimma wata gagarumar nasara a bangaren kirkire-kirkire, inda a ranar 2 ga watan Oktoban 2023 wani dalibinta, dan shekara 28 a duniya, Ibelo Chinemerem, haifaffen garin Akokwa ta jihar Ima ya bai wa kowani da ke yankin mamaki ta hanyar kera jirgi da ya yi tafiya mai nisa a sama kuma ya shafe tsawon mintina bakwai kafin daga bisani ya sauko lami-lafiya.

Wannan abin ban mamakin ya faru ne a filin DCC da ke kusa da babban shataletalen Okpu-na-Egwu da ke kusa da tashar motocin kabu-kabu ta Eastern Mass Transit.

  • Mi’ara Koma Baya-Taylor Ya Koma Alkalancin Gasar ‘Yan Dagaji Ta Kasar Ingila
  • Sojoji Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 2 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Chinemerem, wanda ya kammala sakandarin fasaha ta Akokwa, ya ce, ya fara yunkurin kera jirgi ne tun a shekarar 2014 lokacin yana makaranta amma ya bar makarantar a 2016, sannan sakamakon rashin kudin da zai shiga jami’a domin cigaba da harkokin karatunsa, nan ya yanke shawarar komawa Nnewi a shekarar 2016.

Ya ce, a shekarar 2014 ne ya kera jirginsa na farko, amma jirgin bai tashi sama ba balle ya yi yawo saboda karancin kayayyakin da ya yi amfani da su wajen hadawa.

“Na kera wancan din da Zink, amma kwata-kwata bai tashi sama ba,” ya shaida.

Ya kara da cewa, ya fara cimma nasarara a rayuwarsa ne a Nnewi a shekarar 2020 lokacin da ya samu gagarumin nasarar kera wani jirgi amma a yunkurin tashinsa ya fado ya yi hatsari nan take ya wargaje.

Ya ce, hakan bai sanya ya ji sanyin guiwa ba, hakan ya sake ba shi kwarin guiwa ma har ya sake hada wani a shekarar 2021 da ya tashi har ya yi yawo na tsawon mintina biyu, kuma ya sauko lami-lafiya ba tare da wani matsala ba. Ya kara da cewa, sunan jirgin ‘Cessla’.

Chinemerem, da ke da zama a Uru-Umudim Nnewi, ya shaida cewar ya fara kera babban jirginsa mai suna Biper Tube wata guda da ya wuce.

Ya jero sunayen kayan da ya yi amfani da su wajen hada sabon jirgin nasa da ya daukaki lifafarsa, da cewa, “Na yi amfani da DC na mota, propeller, giya, mai, kumfa, giyan sauka, batiri, mai damar aiki na 2200mah, da zai iya tsawon mintina shida ko bakwai a sama na shawagi.

“Na fara gwagwarmayar hada jirgi ne tun ina dan shekara goma a duniya.

Amma ban taba shiga cikin jirgin ba sai yanzu, ko filin jirgi ma ban taba shiga ba. Kawai ina kallon jirgi ne a talabijin yayin da ke shawagi

a sama.” Chinemerem, ya ce, a halin yanzu haka shi ma’aikacin wucin gadi ne a inda yake aiki domin samun taso sisi domin rufa wa kansa asiri. Ya kara da cewa yana aiki ne a wurin gine-gine, inda daga cikin aikinsa akwai dankan siminti da buluk domin a yi gini da su kuma a biyashi kudin kwadagonsa.

Ya ce, idan da zai samu wadataccen horo da kayayyakin aiki da yake bukata, tabbas zai iya gina jirgin saman da zai yi yawo da shawagi a fadin duniya kuma ya dawo inda ake so lami lafiya.

Ya bayar da bayanin shirinsa na cewa duk da fama da rashin wadataccen kudi, zai cigaba da kere-kere da hada abubuwa musamman jirage domin cimma burin rayuwarsa, ya bada tabbacin cewa idan da zai samu gudunmawar kayan aiki da abubuwan da suka dace zai hada jiragen da za a sha mamakinsu matuka.

Ya yi kira ga masu hannu da shuni da gwamnatoci da su ke taimaka wa matune irinsa masu kaifin basira da baiwa domin su samu damar cimma burikansu na rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Dalilan Da Suka Sanya Dole Nijeriya Ta Rungumi Fasaha Domin Bunkasa Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version