ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Kori Duk Wani Malamin Jami’ar Jihar Kaduna Da Ya Shiga Yajin Aikin ASUU — El-Rufai

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Zan

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai ya yi barazanar korar dukkanin malamin jami’ar jihar Kaduna (KASU) da ya shiga yajin aikin da kungiyar Malaman jami’o’i (ASUU) ke kan yi a halin yanzu.

ASUU dai tun a watan Fabrairu ta shiga yajin aiki kan gaza cika musu bukatunsu daga wajen gwamnatin tarayya. An yi ta kokarin yadda za a yi domin shawo kan yajin aikin amma har yanzu babu wani sakamako mai kyau, inda ko a ranar Litinin ma kungiyoyin Kwadago suka gudanar da jerin gwano a kasa baki daya domin mara wa ASUU ba.

  • ASUU Ta Soki NLC Kan Yin Zanga-Zangar Minti 20 A Anambra
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sace Buhari Da El-Rufai 

Da ya ke magana cikin wani shirin rediyo a Kaduna a ranar Larabar, el-Rufai ya bukaci malaman da su koma ajuzuwansu domin ci gaba da koyar da dalibai domin kauce wa rasa aikinsu.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya ce malaman KASU ba su da wani dalilin shiga wani yajin aiki. Ya kara da cewa ASUU na da matsalolin ne da gwamnatin tarayya ba da jihar ba.

“Mukaddashin Shugaban Jami’ar ya tabbatar min da cewa za su koma bakin aiki na kuma nemi su tabbatar da sun koma din domin da farko na bada umarnin a dakatar da biyansu albashi. Na umarci a bincika duk wanda ya karbi albashi kuma ya shiga yajin aiki dole ya dawo da albashin da ya karba.”

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

“Saboda dokar Nijeriya ya ce babu aiki babu biya. Don haka wannan dokar. Don haka duk wanda ya shiga yajin aiki to babu batun biyanshi albashi. Mun sha fada wa malaman KASU cewa ba su da wata matsala da gwamnatin Jihar Kaduna. Matsalar ASUU matsala ce da gwamnatin tarayya, don haka don meye ma’aikatanmu da ba su da matsala da mu za su shiga yajin aiki.

“Idan hakan ya ci gaba da faruwa, rana daya zan tashi na kori dukkaninsu. Na rantse da Allah. Za mu kori dukkaninsu kuma mu sanar da bukatar daukar ma’aikatan da za su maye gurbinsa a shafukan jaridu. Da zarar suka sake yin irin wannan bayan gargadin da muka ba su. Na rantse da Allah zan kori dukkanin wadanda suka shiga yajin aiki da kin komawa bakin aiki.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Next Post
Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

LABARAI MASU NASABA

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.