• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Kori Duk Wani Malamin Jami’ar Jihar Kaduna Da Ya Shiga Yajin Aikin ASUU — El-Rufai

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Zan Kori Duk Wani Malamin Jami’ar Jihar Kaduna Da Ya Shiga Yajin Aikin ASUU — El-Rufai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai ya yi barazanar korar dukkanin malamin jami’ar jihar Kaduna (KASU) da ya shiga yajin aikin da kungiyar Malaman jami’o’i (ASUU) ke kan yi a halin yanzu.

ASUU dai tun a watan Fabrairu ta shiga yajin aiki kan gaza cika musu bukatunsu daga wajen gwamnatin tarayya. An yi ta kokarin yadda za a yi domin shawo kan yajin aikin amma har yanzu babu wani sakamako mai kyau, inda ko a ranar Litinin ma kungiyoyin Kwadago suka gudanar da jerin gwano a kasa baki daya domin mara wa ASUU ba.

  • ASUU Ta Soki NLC Kan Yin Zanga-Zangar Minti 20 A Anambra
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sace Buhari Da El-Rufai 

Da ya ke magana cikin wani shirin rediyo a Kaduna a ranar Larabar, el-Rufai ya bukaci malaman da su koma ajuzuwansu domin ci gaba da koyar da dalibai domin kauce wa rasa aikinsu.

Gwamnan ya ce malaman KASU ba su da wani dalilin shiga wani yajin aiki. Ya kara da cewa ASUU na da matsalolin ne da gwamnatin tarayya ba da jihar ba.

“Mukaddashin Shugaban Jami’ar ya tabbatar min da cewa za su koma bakin aiki na kuma nemi su tabbatar da sun koma din domin da farko na bada umarnin a dakatar da biyansu albashi. Na umarci a bincika duk wanda ya karbi albashi kuma ya shiga yajin aiki dole ya dawo da albashin da ya karba.”

Labarai Masu Nasaba

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

“Saboda dokar Nijeriya ya ce babu aiki babu biya. Don haka wannan dokar. Don haka duk wanda ya shiga yajin aiki to babu batun biyanshi albashi. Mun sha fada wa malaman KASU cewa ba su da wata matsala da gwamnatin Jihar Kaduna. Matsalar ASUU matsala ce da gwamnatin tarayya, don haka don meye ma’aikatanmu da ba su da matsala da mu za su shiga yajin aiki.

“Idan hakan ya ci gaba da faruwa, rana daya zan tashi na kori dukkaninsu. Na rantse da Allah. Za mu kori dukkaninsu kuma mu sanar da bukatar daukar ma’aikatan da za su maye gurbinsa a shafukan jaridu. Da zarar suka sake yin irin wannan bayan gargadin da muka ba su. Na rantse da Allah zan kori dukkanin wadanda suka shiga yajin aiki da kin komawa bakin aiki.”

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barazanar ‘Yan Bindiga: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Duk Makarantun Jihar

Next Post

Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

Related

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo
Labarai

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

10 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

15 hours ago
Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari
Rahotonni

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

17 hours ago
Alhazan Abuja Sun Gamu Da Tasku Sakamakon Rashin Samun Masaukai Masu Kyau A Saudiyya 
Labarai

Za Mu Kwashe Daukacin Maniyyatan Bana 6000 – Hukumar Alhazan Kano

19 hours ago
Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare
Labarai

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

20 hours ago
Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu
Labarai

Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

22 hours ago
Next Post
Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

LABARAI MASU NASABA

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

June 3, 2023
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Tsarin Wayewar Kan Kasar Sin Mai Dacewa Da Zamani

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Tsarin Wayewar Kan Kasar Sin Mai Dacewa Da Zamani

June 3, 2023
Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Wuraren Al’adun Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Wuraren Al’adun Sin Tana Da Babbar Ma’ana

June 3, 2023
Sin Ta Jaddada Kira Ga Sassan Masu Ruwa Da Tsaki A Rikicin Sudan Da Su Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta

Sin Ta Jaddada Kira Ga Sassan Masu Ruwa Da Tsaki A Rikicin Sudan Da Su Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta

June 3, 2023
Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

June 3, 2023
‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

June 3, 2023
Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

June 3, 2023
Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?

Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?

June 3, 2023
Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Sakataren Tsaron Amurka A Taron Shangri-La

Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Sakataren Tsaron Amurka A Taron Shangri-La

June 3, 2023
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.