• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Mulkin Sojoji Ba Mafita Ba Ne – Hamza Al-Mustapha

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Zanga-zanga: Mulkin Sojoji Ba Mafita Ba Ne – Hamza Al-Mustapha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dogarin tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Marigari Sani Abach, Ham-za Al-Mustapha, ya ce duk da yadda ‘yan Nijeriya suka fusata na kiraye-kirayen kan cewa sojojo karbe mulki a Nijeriya, mulkin soja ba mafita ba ce.

Al-Mustapha, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan halin da kasar ke ciki, ya ce akwai bukatar a daidaita tsarin dimoku-radiyyar Nijeriya domin tunkarar kalubalen da ake fuskanta.

  • Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC
  • Yadda Aljanu Suka Shiga Zanga-zangar Da Aka Yi A Kano – Dakta Kachako  

Ya ce kamata ya yi sojoji su kasance masu bin tsarin dimokuradiyya bisa kwarewa, yana mai jaddada bukatar karfafa sojoji a matsayinsu na wani bangare mai da hankali kan inganta tsaro a kasar nan.

Ya ce, “Sojoji wani bangare ne na dimokuradiyya bayyananne kamar yadda duni-ya take a yau. Amma idan kana da tsarin dimokuradiyya, irin wanda muke aiki da shi na tsarin shugaban kasa. A cikin abubuwan da muka gabatar a baya, ina ada-wa da tsarin shugaban kasa a Nijeriya, misalan da na bayar shi ne, yadda kasashe biyu na kud-da-kud, mafi kusa da mu, wato Ingila da Amurka, daya na tafiyar da tsarin majalisar dokoki, dayan kuma na tafiyar da tsarin shugaban kasa, duk suna da alaka ne da tarihinsu, tare da saukaka wa jama’a, wanda Nijeriya take kwaikwayo.

“Mun kwafi tsarin majalisa, mun canza shi zuwa tsarin shugaban kasa. Dukansu biyun bakon al’ada ne ga al’adunmu, ga tarihinmu, ga asalinmu, fahimtarmu a matsayinmu na al’umma, ta yaya za ku kawo tsari iri daya ku karbe irin naku? ba zai yi aiki ba, zai zama abin kyama.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

GORON JUMA’A 09/05/2025

“Na ba ku wasu misalai, wasu ‘yan siyasa ne suka zo wurina suka ce ka da na fadi haka a fili, ku bari mu ci gaba da gudanar da ayyukanmu kamar yadda muke, amma kuma ni ba zan iya yin wani yaudara ba. Na ce kasar Amurka kasa ce da bakin haure suka zama ‘yan kasa, suna da dokokin da za su kare su kuma tam-bayar da na yi ita ce, a Nijeriya ye dan ci-rani kuma ye asalin dan kasa ne?

“Ta yaya za ku sami tsarin mulki wanda zai kare bakin haure? Wane ne bako a Ni-jeriya? Dukanmu ‘yan kasa ne. Don haka, ya kamata mu tsara tsarinmu da kanmu ba kaikwayon na wasu kasashe ba, dole ne mu sami tsarin dimokuradiyyar da za ta dace da mu. Abin da nake kira kenan a samar, amma batun mulkin soja.”

Sai dai ya ce matasan Nijeriya da suke daga tutocin kasar Rasha sun yi haka ne domin neman mafita, inda suka bukaci da a sake duba hanyar shugabanci domin samun damar magance matsalolin da suke fuskanta.

Al-Mustapha ya ci gaba da cewa shi ba ya goyon bayan zanga-zangar da ake yi a titunan kasar, amma ya jaddada cewa abin da ke da kyau shi ne masu zanga-zangar sun ba da sanarwa kuma duk da dogon sanarwar da suka bayar gwamnati ta kasa biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HamzaJuyin MulkiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Next Post

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Related

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

40 minutes ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

2 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

3 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

4 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

5 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

6 hours ago
Next Post
Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.