ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Mulkin Sojoji Ba Mafita Ba Ne – Hamza Al-Mustapha

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zanga-zanga

Tsohon dogarin tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Marigari Sani Abach, Ham-za Al-Mustapha, ya ce duk da yadda ‘yan Nijeriya suka fusata na kiraye-kirayen kan cewa sojojo karbe mulki a Nijeriya, mulkin soja ba mafita ba ce.

Al-Mustapha, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan halin da kasar ke ciki, ya ce akwai bukatar a daidaita tsarin dimoku-radiyyar Nijeriya domin tunkarar kalubalen da ake fuskanta.

  • Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC
  • Yadda Aljanu Suka Shiga Zanga-zangar Da Aka Yi A Kano – Dakta Kachako  

Ya ce kamata ya yi sojoji su kasance masu bin tsarin dimokuradiyya bisa kwarewa, yana mai jaddada bukatar karfafa sojoji a matsayinsu na wani bangare mai da hankali kan inganta tsaro a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Sojoji wani bangare ne na dimokuradiyya bayyananne kamar yadda duni-ya take a yau. Amma idan kana da tsarin dimokuradiyya, irin wanda muke aiki da shi na tsarin shugaban kasa. A cikin abubuwan da muka gabatar a baya, ina ada-wa da tsarin shugaban kasa a Nijeriya, misalan da na bayar shi ne, yadda kasashe biyu na kud-da-kud, mafi kusa da mu, wato Ingila da Amurka, daya na tafiyar da tsarin majalisar dokoki, dayan kuma na tafiyar da tsarin shugaban kasa, duk suna da alaka ne da tarihinsu, tare da saukaka wa jama’a, wanda Nijeriya take kwaikwayo.

“Mun kwafi tsarin majalisa, mun canza shi zuwa tsarin shugaban kasa. Dukansu biyun bakon al’ada ne ga al’adunmu, ga tarihinmu, ga asalinmu, fahimtarmu a matsayinmu na al’umma, ta yaya za ku kawo tsari iri daya ku karbe irin naku? ba zai yi aiki ba, zai zama abin kyama.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

“Na ba ku wasu misalai, wasu ‘yan siyasa ne suka zo wurina suka ce ka da na fadi haka a fili, ku bari mu ci gaba da gudanar da ayyukanmu kamar yadda muke, amma kuma ni ba zan iya yin wani yaudara ba. Na ce kasar Amurka kasa ce da bakin haure suka zama ‘yan kasa, suna da dokokin da za su kare su kuma tam-bayar da na yi ita ce, a Nijeriya ye dan ci-rani kuma ye asalin dan kasa ne?

“Ta yaya za ku sami tsarin mulki wanda zai kare bakin haure? Wane ne bako a Ni-jeriya? Dukanmu ‘yan kasa ne. Don haka, ya kamata mu tsara tsarinmu da kanmu ba kaikwayon na wasu kasashe ba, dole ne mu sami tsarin dimokuradiyyar da za ta dace da mu. Abin da nake kira kenan a samar, amma batun mulkin soja.”

Sai dai ya ce matasan Nijeriya da suke daga tutocin kasar Rasha sun yi haka ne domin neman mafita, inda suka bukaci da a sake duba hanyar shugabanci domin samun damar magance matsalolin da suke fuskanta.

Al-Mustapha ya ci gaba da cewa shi ba ya goyon bayan zanga-zangar da ake yi a titunan kasar, amma ya jaddada cewa abin da ke da kyau shi ne masu zanga-zangar sun ba da sanarwa kuma duk da dogon sanarwar da suka bayar gwamnati ta kasa biya musu bukatocinsu.

Zanga-zanga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.