• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Mulkin Sojoji Ba Mafita Ba Ne – Hamza Al-Mustapha

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai
0
Zanga-zanga: Mulkin Sojoji Ba Mafita Ba Ne – Hamza Al-Mustapha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dogarin tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Marigari Sani Abach, Ham-za Al-Mustapha, ya ce duk da yadda ‘yan Nijeriya suka fusata na kiraye-kirayen kan cewa sojojo karbe mulki a Nijeriya, mulkin soja ba mafita ba ce.

Al-Mustapha, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan halin da kasar ke ciki, ya ce akwai bukatar a daidaita tsarin dimoku-radiyyar Nijeriya domin tunkarar kalubalen da ake fuskanta.

  • Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC
  • Yadda Aljanu Suka Shiga Zanga-zangar Da Aka Yi A Kano – Dakta Kachako  

Ya ce kamata ya yi sojoji su kasance masu bin tsarin dimokuradiyya bisa kwarewa, yana mai jaddada bukatar karfafa sojoji a matsayinsu na wani bangare mai da hankali kan inganta tsaro a kasar nan.

Ya ce, “Sojoji wani bangare ne na dimokuradiyya bayyananne kamar yadda duni-ya take a yau. Amma idan kana da tsarin dimokuradiyya, irin wanda muke aiki da shi na tsarin shugaban kasa. A cikin abubuwan da muka gabatar a baya, ina ada-wa da tsarin shugaban kasa a Nijeriya, misalan da na bayar shi ne, yadda kasashe biyu na kud-da-kud, mafi kusa da mu, wato Ingila da Amurka, daya na tafiyar da tsarin majalisar dokoki, dayan kuma na tafiyar da tsarin shugaban kasa, duk suna da alaka ne da tarihinsu, tare da saukaka wa jama’a, wanda Nijeriya take kwaikwayo.

“Mun kwafi tsarin majalisa, mun canza shi zuwa tsarin shugaban kasa. Dukansu biyun bakon al’ada ne ga al’adunmu, ga tarihinmu, ga asalinmu, fahimtarmu a matsayinmu na al’umma, ta yaya za ku kawo tsari iri daya ku karbe irin naku? ba zai yi aiki ba, zai zama abin kyama.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

“Na ba ku wasu misalai, wasu ‘yan siyasa ne suka zo wurina suka ce ka da na fadi haka a fili, ku bari mu ci gaba da gudanar da ayyukanmu kamar yadda muke, amma kuma ni ba zan iya yin wani yaudara ba. Na ce kasar Amurka kasa ce da bakin haure suka zama ‘yan kasa, suna da dokokin da za su kare su kuma tam-bayar da na yi ita ce, a Nijeriya ye dan ci-rani kuma ye asalin dan kasa ne?

“Ta yaya za ku sami tsarin mulki wanda zai kare bakin haure? Wane ne bako a Ni-jeriya? Dukanmu ‘yan kasa ne. Don haka, ya kamata mu tsara tsarinmu da kanmu ba kaikwayon na wasu kasashe ba, dole ne mu sami tsarin dimokuradiyyar da za ta dace da mu. Abin da nake kira kenan a samar, amma batun mulkin soja.”

Sai dai ya ce matasan Nijeriya da suke daga tutocin kasar Rasha sun yi haka ne domin neman mafita, inda suka bukaci da a sake duba hanyar shugabanci domin samun damar magance matsalolin da suke fuskanta.

Al-Mustapha ya ci gaba da cewa shi ba ya goyon bayan zanga-zangar da ake yi a titunan kasar, amma ya jaddada cewa abin da ke da kyau shi ne masu zanga-zangar sun ba da sanarwa kuma duk da dogon sanarwar da suka bayar gwamnati ta kasa biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HamzaJuyin MulkiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Next Post

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

7 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

8 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.