• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami’ai 30,000 Faɗin Nijeriya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Tsaro, Manyan Labarai
0
Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami’ai 30,000 Faɗin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar tsaro ta NSCDC, Dr. Audi, ya umarci a rarraba jami’ai 30,000 a duk faɗin ƙasa kafin zanga-zangar da aka shirya gudanarwa daga ranar 1 zuwa 10 ga Agusta. A cikin taron gaggawa da aka gudanar a Shalƙwatar NSCDC a Abuja, Dr. Audi ya jaddada buƙatar jami’an su kasance masu ƙwarewa da ladabi da kuma bin ƙa’idojin.

Ya jaddada cewa yayin da ‘yan ƙasa ke da haƙƙin yin zanga-zanga cikin lumana, ba su da haƙƙin lalata kadarorin gwamnati. Jami’an da za a tura za su kasance ƙarƙashin kulawar shugabannin yanki da kwamandojin Jihohi a jihohi 36 da FCT.

  • Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja
  • Ba Zamu Lamunci Zanga-Zangar Tashin Hankali Ba – IGP 

Dr. Audi ya gargaɗi jami’an da su guji duk wani aiki na zalunci ko take haƙƙin ɗan adam, yana jaddada cewa NSCDC ba za ta lamunci duk wani abu da zai ɓata sunanta ba. Ya bayyana muhimmancin kare muhimman kadarorin ƙasa da gine-ginen gwamnati daga yiwuwar lalata su yayin zanga-zangar.

Bugu da ƙari, Dr. Audi ya yi kira ga matasan Nijeriya da su guji ayi amfani da su wajen aikata duk wani mummunan aiki, yana ba da shawarar tattaunawa maimakon ayyukan assha da za su jawo da na sani. Ya jaddada aniyar hukumar na haɗa kai da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da zaman lafiya da ƙarfafa tsarin tsaron ƙasa.

A cikin jawabin sa, Dr. Audi ya yi kira da a yi zanga-zangar cikin lumana idan dole sai an yi, yana tunatar da zanga-zangar baya da ta haifar da tashin hankali, da lalata dukiya, da kuma rasa rayuka.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Ya umarci jami’ai da su tabbatar zanga-zangar ta kasance cikin lumana kuma su kare gine-ginen gwamnati daga ‘yan daba. Shugaban NSCDC ya tabbatar da cewa hukumar tana da ƙwazo wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, tare da inganta zaman lafiya da kuma bunƙasa tsaron ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Civil DefenceNSCDCProtestZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaurar Da Mutane Dubu 3 Sakamakon Fashewar Madatsar Ruwa A Gundumar Xiangtan Ta Sin

Next Post

Arsenal Ta Kammala Ɗaukar Riccardo Calafiori Daga Bologna

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

7 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

11 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

17 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

21 hours ago
Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

2 days ago
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Manyan Labarai

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

2 days ago
Next Post
Arsenal Ta Kammala Ɗaukar Riccardo Calafiori Daga Bologna

Arsenal Ta Kammala Ɗaukar Riccardo Calafiori Daga Bologna

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.