• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan tirjiya na karin kudin wutan lantarki da hukumomi suka yi a Nijeriya a watan da ta gabata, kungiyar kwadago a Nijeriya sun dukufa wajen gudanar da zanga-zanga tare da neman dole a canye zancen karin kudin wuta da kuma magance matsalar wutar lantarki.

Rahotonni sun yi nuni da cewa kungiyar kwadago sun rufe dukkanin ofisoshin kamfanonin rarraba wutar lantaki guda 11 da babban ofishin hukumar kula da wutar lantarki ta kasa a yayin da suka tsunduma gudanar da zanga-zangar na ranar Litinin.

  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi
  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu

Shugaban kungiyar kwadago, Joe Ajaero shi ne ya jagoranci zanga-zangar a Abuja har zuwa ga ministan wuta da kuma shalkwatar hukumar kula da lamarin wuta a Nijeriya (NERC).

 Sannan an rufe ofishin kamfanin rarraba wutar lantarki tare da hana ma’aikata shiga domin gudanar da aiki.

 Bugu da kari, haka zancen yake a sauran ofisoshin kamfanin da ke jihohi da suka hada da na Kwara, Legas, Kaduna, Filato, Inugu, Sakkwato, Bauchi da sauran ofisoshi da suke sassan kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

Ajaero, yayin zanga-zangar, ya ce akwai bukatar NERC ta sake nazarin matakan da suka bi wajen karin kudin wuta. Ya ce, karin kudin ya janyo tashin farashin ababe da dama musamman kayan abinci.

 A martaninta kan zanga-zangar na kwana guda, gwamnatin Nijeriya ta ce ta fara tattaunawa da kungiyar kwadago kan lamarin.

Kakakin ministan wuta a Nijeriya, Florence Eke, ta shaida wa majiyarmu ta wayar tarho cewa bayan zanga-zangar ma’aikatan, gwamnatin tarayya ta hannun babban sakatare, Mista Mamman Mahmuda, ya kira taron ganawa da kungiyar kwadago a mako mai zuwa, ganawar da zai hada har da masu ruwa da tsaki domin lalubo bakin zaren matsalar.

“Ma’aikatar wuta za ta gayyaci dukkanin masu ruwa da tsaki domin nemo mafita kan wannan batun a mako mai zuwa,” ta shaida.

Mai magana da yawun kungiyar kwadago, Benson Upah, ya ce, ya kamata ne gwamnati ta tuntubi masu ruwa da tsaki tun kafin ta aiwatar da manufar karin kudin wutar a ranar 3 ga watan Afrilu.

Ya tabbatar da cewa zanga-zanga da suka fara muddin gwamnati ta kasa komawa baya kan matakinta na karin kudin lantarki za su ci gaba.

Idan za a tuna dai a watan Afrilun 2024 ne hukumar kula da wutar lantarki a Nijeriya ta sanar da karin kudin lantarki da kaso 240 ga kwastomomin da ke amfani da rukunin A.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiKarin Kudin WutaLantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Philippines Da Ta Dakatar Da Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin

Next Post

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Related

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya
Manyan Labarai

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

35 minutes ago
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro
Labarai

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

2 hours ago
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano
Manyan Labarai

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

4 hours ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

5 hours ago
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

7 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

9 hours ago
Next Post
Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

September 2, 2025
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

September 2, 2025
Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

September 2, 2025
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

September 2, 2025
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.