• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar Minna: Shugaba Tinubu Ya Ba Da Umarnin A Sassauta Farashin Kayan Abinci – Idris

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zanga-zangar da mata suka gudanar a Minna, babban birnin Jihar Neja, dangane da tsadar kayan abinci da kuma tsadar rayuwa baki ɗaya, ta zaburar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu har ya ba da umarni ga hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta daƙile hauhawar farashin kayan abinci a faɗin ƙasar nan.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan tashi daga taron da Kwamitin Shugaban Ƙasa kan bada Agajin gaggawa na raba abinci ya yi a ranar Talata a Abuja.

  • An Hada Rukunin Karshe Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ta Gina A Uganda Da Layin Wutar Lantarki Na Kasa
  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Kwamitin Asusun Samar Da Tallafin Tsaro

Idris ya ce Shugaban Ƙasa ya damu sosai dangane da yadda abinci ke ƙara tsadar nesanta kan sa daga talakawa a faɗin ƙasar nan.

Ministan ya ce, zanga-zangar da mata suka yi a Minna dangane da tsadar abinci, ya zaburar da Gwamnatin kan ɗaukar wasu matakai domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun samu sauƙi da rahusa, ta yadda abinci ba zai riƙa neman gagarar su ba.

Ya ƙara da cewa kwamitin zai ci gaba da yin taro har zuwa ranar Alhamis.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

Ya ce tuni aka fara ɗaukar wasu muhimman matakai domin rage wa jama’a raɗaɗin tsadar rayuwa da tsadar farashin kayan abinci.

Ya ce: “Daga cikin matakan akwai gaggauta fito da kayan abincin da gwamnatin tarayya ta tanadar a rumbunan ajiyar abincin gwamnati da ke faɗin ƙasar nan.

“Sannan kuma gwamnati na tattaunawa da manyan masu sarrafawa ko cashe kayan abinci da manyan ‘yan kasuwar kayan abinci da kayan masarufi, domin tantance adadin abin da suke da shi a ajiye a rumbunan ajiyar su.

“Dalilin yin hakan shi ne gwamnati na so ta gaggauta shiga cikin lamarin domin abinci ya wadata ga ‘yan Nijeriya.”

Sai dai kuma ya yi tsokacin cewa, gwamnati na sane akwai wasu marasa kishin kasa kuma marasa tausayi da ke ɓoye abinci domin su sayar idan ya yi tsada sosai.

“Gwamnati ba za ta zura ido ‘yan Nijeriya na fama da tsadar kayan abinci ba, alhali wasu na haifar da ƙarancin sa. Don haka ina roƙon jama’a su fahimci irin damuwar gwamnati da kuma ƙoƙarin da ta ke yi.

“Yayin da aka kammala waɗannan tarukan, za mu fito da sanarwa dangane da matsayi da matakan da gwamnati ta ɗauka.”

Taron ya samu halartar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila; Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Yemi Cardoso; Ministan Harkokin Kuɗaɗe, Wale Edun, da Mashawarcin Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu.

Sauran sun haɗa da Ministan Noma, Abubakar Kyari, na Kasafin Kuɗaɗe Da Tsare-tsare, Atiku Bagudu, sai kuma Ƙananan Ministocin Gona da FCT Abuja, Sabi Abdullahi da Mariya Mahmood.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaTsadar RayuwaZanga-zangar adawa da yunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Nangolo Mbumba Murnar Zama Shugaban Kasar Namibiya

Next Post

Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

Related

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro
Labarai

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro

59 minutes ago
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano
Manyan Labarai

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

3 hours ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 hours ago
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

6 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Labarai

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

9 hours ago
Next Post
Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

September 2, 2025
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro

September 2, 2025
Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

September 2, 2025
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

September 2, 2025
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.