• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar China ta kasance ta gaba gaba a fannin noman tumatir a duniya. Musamman a jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar, an fi noman tumatir sabo da jihar tana da wani irin yanayi wanda tumatir yake bukata. Sama da kashi 30% na yawan tumarin da ake samarwa a kasuwar duniya yana fitowa ne daga China. Harkar noman tumatir yana habaka cikin sauri, musamman idan aka yi la’akari da yadda nau’in tumatirin China ya fi na sauran kasashe inganci. Sabo da kyawo da inganci da kuma rahusa ya sanya tumatirin kasar China ya samu karbuwa a yawancin gidajen abinci na kasashen yammacin duniya.  

Sakamakon rikice-rikice da wasu yankuna na duniya suka samu kansu a ciki ya sanya farashin amfanin gona ya yi matukar hauhawa a kasuwannin duniya, ciki kuwa har da tumatir. To amma duk da hauhawar farashin, ana samun tumatirin kasar China cikin sauki da rahusa, abin da ya sanya ya kara samun karbuwa a kasuwar duniya.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bikin Kaddamar Da Aikin Layin Dogo Na Sin- Kyrgyzstan-Uzbekistan
  • Ma’aikatar Kananan Hukumomi A Zamfara Ta Gabatar Da Bitar Kasafin Kudin Kananan Hukumomi 

Wannan lamari na karbuwar da tumatirin China ya samu a duniya ya tsonewa Amerika da kasashen yammaci ido, har ta kai ga suna kulla makirci da yada karerayi game da tumatirin na kasar China, inda suke cewa wai China na amfani da tsarin tursasawa da bautarwa a gonakin tumatir dake jihar Xinjiang. Wasu kafafen yada labaru na yammcin duniya, wadanda su ne karnukan farautar Turai da Amerika suna yayata cewa wai ana tursasawa musulmi ’yan kabilar Uygur suna aikin bauta a gonakin tumatir na lardin Xinjiang.

Irin wadannan karerayi da kafafen yada labarun na Turai ke yadawa, ko kadan babu kamshin gaskiya a cikinsu, illa iyaka hassada ce kawai da ganin kyashi bisa ga yadda kasar ta China take samun ci gaba a fasahar noma.

A bayyane take cewa irin ci gaba da China ta samu a fannin fasahar noma, ba ta bukatar yin amfani da mutane a matsayin leburori, ballantama a ce ta tursasa masu yin aikin karfi a gonakin tumatir. Domin kuwa tun daga matakin dashe har zuwa matakin girbi, na’ura ce ke yin komai. Aikin da leburori 150 za su yi a cikin yini daya, na’ura guda za ta yi shi a cikin yini daya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Akwai wasu ‘yan tsirarrun mutane da irin wadannan kafafen yada labaru na yammaci suke ba su kudi domin su yi ikirarin cewa su al’ummar Xinjiang ne, a yi hira da su, inda za su rinka yin ikirarin cewa mahukunta a China suna tilasta masu aikin bauta a gonakin tumatir a jihar Xinjiang, alhali kuwa irin wadannan mutane ko hanyar Xinjiang ba su sani ba.

Kafafen yada labarun na yammaci wadanda ke babatu kare hakkin dan Adam, sun kasance masu kara jefa mutane cikin rashin aikin yi da talauci. Babu irin kokarin da irin wadannan kafafen yada labaru na kasashen yammaci ba su yi ba na yin batanci ga kasar China, amma duk a banza. Misali, akwai wata kafar yada labaru ta yammaci da ta kirkiro wani shiri na musamman kan bin diddigin inda ake sayar da tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang. Sun bi masana’antun sarrafa tumatirin gwangwani, kamar Petti da Derica, suna daukar samafari domin yin gwaji ko akwai nau’in tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang, amma sakamakon duk gwaje-gwajen nasu bai zo daidai da hakikanin gaskiyar abin da suke zargi ba.

Sabo da haka, batun bautar da leburori, ko kuma tilasta masu yin aikin karfi a gonakin tumatir a jihar Xinjiang magana ce wadda hankali ba zai dauka ba, musamman idan aka yi la’akari da dokokin da ke kare hakkin leburori wadanda China ke bi sau da kafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bikin Kaddamar Da Aikin Layin Dogo Na Sin- Kyrgyzstan-Uzbekistan

Next Post

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

19 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

20 hours ago
Next Post
Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.