• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Bunkasa Aikin Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA), ta horar da manoman Wake tare da ba su kayan aiki; don kara habaka nomansu.

Manoman da suka amfana da horon, sun bayyana jin dadinsu musamman ta fuskar ba su sabon Irin Wake da aka yi; domin amfanuwarsu.

  • Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500
  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Manajan Darakta na Hukumar ta KNARDA, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana cewa, Hukumar tasa a karkashin shirin aikin bunkasa aikin noma da Bankin Musulunci na Bunkasa Aikin na Noma (IsDB), tare da tallafin Shirin Inganta Rayuwar Alumma (LLF) ne suka zuba kudede tare da raba wa manoman sabon Irin na Wake.

Kurawa ya sanar da cewa, an raba wa manoman Irin ne, domin kara habaka noman Wake da kuma bunkasa girbinsa a jihar.

Manajan ya bayyana haka ne, a jawabinsa yayin samar da wannan dauki a kauyen Riga Fada da ke Karamar Hukumar Kumbotso a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

A cewar Kurawan, an samu nasarori da dama a karkashin wannan aiki, inda ya kara da cewa, kamar sauran sassan Nijeriya; su ma manoman da ke Jihar Kano, sun samu bayanai; musamman a kan noman rani.

Shi ma a nasa jawabin, wani jami’i a hukumar ta KNARDA Muhammad Ahmad Nahannu ya bayyana cewa, sabon Irin Waken; na samar da girbi mai yawa fiye da Irin Waken da manoman suka saba shukawa, wanda ya kai kashi goma na rubun da ake samu a girbin.

Ahmad ya kara da cewa, sama da rukunin al’umma 258 da suka hada da mata 25 daga kowanne cikin rukuni, sun amfana da wannan tallafi daban-daban na wannan aiki.

Shi kuwa, Ko’odinetan aikin na KSADP a Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba ya bayyana cewa, Gwamnati ce ke taimaka wa aikin, musamman don kara habaka fannin aikin noma ta hanyar bayar da tallafin kayan aikin noma, bayar da rancen noma, sama wa manoma kasuwa da sauran makamantansu.

Daya daga cikin manoman da suka amfana da tallafin, Malam Auwal Isah Kumbotso ya bayyna cewa, bisa wannan ci gaba da aka sama musu a karkashin wannan aiki, nan ba da jimawa ba; Jihar Kano za ta zama cibiyar noman Wake.

Kumbotso ya kara da cewa, bisa wannan mayar da hankali da aka yi, hakan ya nuna cewa, gwamnatin jihar za a kara nuna sha’awa a aikin noma fiye da yadda ake da sha’awarsa a baya.

A cewarsa,“Mun gamsu da sabon Irin Waken da aka raba mana, domin Iri da aka yi gwajinsa, mahukunta sun aminta da shi”.

Ya kara da cewa, daukacin wadanda suka amfana da sabon Irin, mun tabbatar da hakan domin sakamakon da muka samu daga yin amfani da sabon Irin, mun gamsu da haka.

Ya sanar da cewa, a matsayina na manomi; zan iya bayar da shedar cewa, girbin da na yi na sabon Waken sau biyu; ya rubanya girbin da na yi a bara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?

Next Post

Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

1 day ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.