ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Knarda

Hukumar Bunkasa Aikin Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA), ta horar da manoman Wake tare da ba su kayan aiki; don kara habaka nomansu.

Manoman da suka amfana da horon, sun bayyana jin dadinsu musamman ta fuskar ba su sabon Irin Wake da aka yi; domin amfanuwarsu.

  • Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500
  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Manajan Darakta na Hukumar ta KNARDA, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana cewa, Hukumar tasa a karkashin shirin aikin bunkasa aikin noma da Bankin Musulunci na Bunkasa Aikin na Noma (IsDB), tare da tallafin Shirin Inganta Rayuwar Alumma (LLF) ne suka zuba kudede tare da raba wa manoman sabon Irin na Wake.

ADVERTISEMENT

Kurawa ya sanar da cewa, an raba wa manoman Irin ne, domin kara habaka noman Wake da kuma bunkasa girbinsa a jihar.

Manajan ya bayyana haka ne, a jawabinsa yayin samar da wannan dauki a kauyen Riga Fada da ke Karamar Hukumar Kumbotso a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

A cewar Kurawan, an samu nasarori da dama a karkashin wannan aiki, inda ya kara da cewa, kamar sauran sassan Nijeriya; su ma manoman da ke Jihar Kano, sun samu bayanai; musamman a kan noman rani.

Shi ma a nasa jawabin, wani jami’i a hukumar ta KNARDA Muhammad Ahmad Nahannu ya bayyana cewa, sabon Irin Waken; na samar da girbi mai yawa fiye da Irin Waken da manoman suka saba shukawa, wanda ya kai kashi goma na rubun da ake samu a girbin.

Ahmad ya kara da cewa, sama da rukunin al’umma 258 da suka hada da mata 25 daga kowanne cikin rukuni, sun amfana da wannan tallafi daban-daban na wannan aiki.

Shi kuwa, Ko’odinetan aikin na KSADP a Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba ya bayyana cewa, Gwamnati ce ke taimaka wa aikin, musamman don kara habaka fannin aikin noma ta hanyar bayar da tallafin kayan aikin noma, bayar da rancen noma, sama wa manoma kasuwa da sauran makamantansu.

Daya daga cikin manoman da suka amfana da tallafin, Malam Auwal Isah Kumbotso ya bayyna cewa, bisa wannan ci gaba da aka sama musu a karkashin wannan aiki, nan ba da jimawa ba; Jihar Kano za ta zama cibiyar noman Wake.

Kumbotso ya kara da cewa, bisa wannan mayar da hankali da aka yi, hakan ya nuna cewa, gwamnatin jihar za a kara nuna sha’awa a aikin noma fiye da yadda ake da sha’awarsa a baya.

A cewarsa,“Mun gamsu da sabon Irin Waken da aka raba mana, domin Iri da aka yi gwajinsa, mahukunta sun aminta da shi”.

Ya kara da cewa, daukacin wadanda suka amfana da sabon Irin, mun tabbatar da hakan domin sakamakon da muka samu daga yin amfani da sabon Irin, mun gamsu da haka.

Ya sanar da cewa, a matsayina na manomi; zan iya bayar da shedar cewa, girbin da na yi na sabon Waken sau biyu; ya rubanya girbin da na yi a bara.

Knarda
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
Knarda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.