ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Knarda

Hukumar Bunkasa Aikin Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA), ta horar da manoman Wake tare da ba su kayan aiki; don kara habaka nomansu.

Manoman da suka amfana da horon, sun bayyana jin dadinsu musamman ta fuskar ba su sabon Irin Wake da aka yi; domin amfanuwarsu.

  • Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500
  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Manajan Darakta na Hukumar ta KNARDA, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana cewa, Hukumar tasa a karkashin shirin aikin bunkasa aikin noma da Bankin Musulunci na Bunkasa Aikin na Noma (IsDB), tare da tallafin Shirin Inganta Rayuwar Alumma (LLF) ne suka zuba kudede tare da raba wa manoman sabon Irin na Wake.

ADVERTISEMENT

Kurawa ya sanar da cewa, an raba wa manoman Irin ne, domin kara habaka noman Wake da kuma bunkasa girbinsa a jihar.

Manajan ya bayyana haka ne, a jawabinsa yayin samar da wannan dauki a kauyen Riga Fada da ke Karamar Hukumar Kumbotso a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

A cewar Kurawan, an samu nasarori da dama a karkashin wannan aiki, inda ya kara da cewa, kamar sauran sassan Nijeriya; su ma manoman da ke Jihar Kano, sun samu bayanai; musamman a kan noman rani.

Shi ma a nasa jawabin, wani jami’i a hukumar ta KNARDA Muhammad Ahmad Nahannu ya bayyana cewa, sabon Irin Waken; na samar da girbi mai yawa fiye da Irin Waken da manoman suka saba shukawa, wanda ya kai kashi goma na rubun da ake samu a girbin.

Ahmad ya kara da cewa, sama da rukunin al’umma 258 da suka hada da mata 25 daga kowanne cikin rukuni, sun amfana da wannan tallafi daban-daban na wannan aiki.

Shi kuwa, Ko’odinetan aikin na KSADP a Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba ya bayyana cewa, Gwamnati ce ke taimaka wa aikin, musamman don kara habaka fannin aikin noma ta hanyar bayar da tallafin kayan aikin noma, bayar da rancen noma, sama wa manoma kasuwa da sauran makamantansu.

Daya daga cikin manoman da suka amfana da tallafin, Malam Auwal Isah Kumbotso ya bayyna cewa, bisa wannan ci gaba da aka sama musu a karkashin wannan aiki, nan ba da jimawa ba; Jihar Kano za ta zama cibiyar noman Wake.

Kumbotso ya kara da cewa, bisa wannan mayar da hankali da aka yi, hakan ya nuna cewa, gwamnatin jihar za a kara nuna sha’awa a aikin noma fiye da yadda ake da sha’awarsa a baya.

A cewarsa,“Mun gamsu da sabon Irin Waken da aka raba mana, domin Iri da aka yi gwajinsa, mahukunta sun aminta da shi”.

Ya kara da cewa, daukacin wadanda suka amfana da sabon Irin, mun tabbatar da hakan domin sakamakon da muka samu daga yin amfani da sabon Irin, mun gamsu da haka.

Ya sanar da cewa, a matsayina na manomi; zan iya bayar da shedar cewa, girbin da na yi na sabon Waken sau biyu; ya rubanya girbin da na yi a bara.

Knarda
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Knarda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.