ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
China

Kasar China ta kasance ta gaba gaba a fannin noman tumatir a duniya. Musamman a jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar, an fi noman tumatir sabo da jihar tana da wani irin yanayi wanda tumatir yake bukata. Sama da kashi 30% na yawan tumarin da ake samarwa a kasuwar duniya yana fitowa ne daga China. Harkar noman tumatir yana habaka cikin sauri, musamman idan aka yi la’akari da yadda nau’in tumatirin China ya fi na sauran kasashe inganci. Sabo da kyawo da inganci da kuma rahusa ya sanya tumatirin kasar China ya samu karbuwa a yawancin gidajen abinci na kasashen yammacin duniya.  

Sakamakon rikice-rikice da wasu yankuna na duniya suka samu kansu a ciki ya sanya farashin amfanin gona ya yi matukar hauhawa a kasuwannin duniya, ciki kuwa har da tumatir. To amma duk da hauhawar farashin, ana samun tumatirin kasar China cikin sauki da rahusa, abin da ya sanya ya kara samun karbuwa a kasuwar duniya.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bikin Kaddamar Da Aikin Layin Dogo Na Sin- Kyrgyzstan-Uzbekistan
  • Ma’aikatar Kananan Hukumomi A Zamfara Ta Gabatar Da Bitar Kasafin Kudin Kananan Hukumomi 

Wannan lamari na karbuwar da tumatirin China ya samu a duniya ya tsonewa Amerika da kasashen yammaci ido, har ta kai ga suna kulla makirci da yada karerayi game da tumatirin na kasar China, inda suke cewa wai China na amfani da tsarin tursasawa da bautarwa a gonakin tumatir dake jihar Xinjiang. Wasu kafafen yada labaru na yammcin duniya, wadanda su ne karnukan farautar Turai da Amerika suna yayata cewa wai ana tursasawa musulmi ’yan kabilar Uygur suna aikin bauta a gonakin tumatir na lardin Xinjiang.

ADVERTISEMENT

Irin wadannan karerayi da kafafen yada labarun na Turai ke yadawa, ko kadan babu kamshin gaskiya a cikinsu, illa iyaka hassada ce kawai da ganin kyashi bisa ga yadda kasar ta China take samun ci gaba a fasahar noma.

A bayyane take cewa irin ci gaba da China ta samu a fannin fasahar noma, ba ta bukatar yin amfani da mutane a matsayin leburori, ballantama a ce ta tursasa masu yin aikin karfi a gonakin tumatir. Domin kuwa tun daga matakin dashe har zuwa matakin girbi, na’ura ce ke yin komai. Aikin da leburori 150 za su yi a cikin yini daya, na’ura guda za ta yi shi a cikin yini daya.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Akwai wasu ‘yan tsirarrun mutane da irin wadannan kafafen yada labaru na yammaci suke ba su kudi domin su yi ikirarin cewa su al’ummar Xinjiang ne, a yi hira da su, inda za su rinka yin ikirarin cewa mahukunta a China suna tilasta masu aikin bauta a gonakin tumatir a jihar Xinjiang, alhali kuwa irin wadannan mutane ko hanyar Xinjiang ba su sani ba.

Kafafen yada labarun na yammaci wadanda ke babatu kare hakkin dan Adam, sun kasance masu kara jefa mutane cikin rashin aikin yi da talauci. Babu irin kokarin da irin wadannan kafafen yada labaru na kasashen yammaci ba su yi ba na yin batanci ga kasar China, amma duk a banza. Misali, akwai wata kafar yada labaru ta yammaci da ta kirkiro wani shiri na musamman kan bin diddigin inda ake sayar da tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang. Sun bi masana’antun sarrafa tumatirin gwangwani, kamar Petti da Derica, suna daukar samafari domin yin gwaji ko akwai nau’in tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang, amma sakamakon duk gwaje-gwajen nasu bai zo daidai da hakikanin gaskiyar abin da suke zargi ba.

Sabo da haka, batun bautar da leburori, ko kuma tilasta masu yin aikin karfi a gonakin tumatir a jihar Xinjiang magana ce wadda hankali ba zai dauka ba, musamman idan aka yi la’akari da dokokin da ke kare hakkin leburori wadanda China ke bi sau da kafa.

China
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
China
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.