• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da kotun daukaka kara ke ci gaba da zartar da hukunci game da shari’o’in zabe da aka daukaka daga kotunan sauraron kararrakin zabe, hukuncin ya haifar da cacar baki a tsakanin ‘yan adawa da gwamnati, wanda wasu suka fara zargin ana yi wa dimokuradiyyar Nijeriya kafar angulu.

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayyana cewa dimokuradiyyar Nijeriya na fuskantar barazana karkashin gwamnatin APC, wanda a yanzu a bangaren shari’ar Nijeriya na sayar da hukunci kudi-a-hannu.

  • Zargin Baɗala: Hisba Ta Kama Mata Da Maza A Zamfara
  • Zaben Kano: Abba Ya Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli

Atiku ya jaddada damuwarsa kan dorewar dimokuradiyyar Nijeriya da ke fuskantar barazana na yadda jam’iyya mai mulki ke amfani da kotuna waje tsege gwamnonin ‘yan jam’iyyar adawa a jihohin Nijeriya.

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe ya fitar, ya ce ana raunata ‘yan adawa a Nijeriya ta hanyar yin magudin zabe da kuma amfani da kotuna ana amshe kujerunsu.

Ya kara da cewa, “Abin da ya fi daukar hankali shi ne, jihohin da kotuna suka yanke hukuncin cire gwamnonin dukkansu na jam’iyyun adawa ne. Tun daga Kano, Zamfara zuwa Filato, inda muke ganin cewa jam’iyya mai mulki ta kasa yin nasara a wadannan jihohi a lokacin zabe, amma kuma yanzu tana amsa a kotu.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

“Wadannan alamu ne masu barazana ga harkokin zabe da bangaren shari’a tare da tabbatar da cewa dimokuradiyyarmu ta lalace. A bayyana yake jam’iyya mai mulki tana gudanar da mummunar akida ta kwace mulki daga hannun ‘yan adawa.

“Abin da ya fi daukar hankali shi ne, abin da ke faruwa a yanzu a game da zaben gwamnan Filato, wanda tun farko dan majalisar APC a wani faifan bidiyo ya yi barazanar cewa jam’iyya mai mulki za ta bi tsarin shari’a don tabbatar da nasararta a kotuna.

“Saboda haka, yana nufin cewa zamanin da muke ciki a zahiri abin tsoro ne, kuma akwai jan aiki a gabanmu wajen ceto dimokuradiyyarmu daga hannun wadannan masu neman mulki ko ta wani hali.”

Sai dai Atiku ya ce ya yi mamakin abin da ke faruwa a yanzu, inda ya ce a Jihar Legas inda Shugaba kas, Bola Tinubu ya fito ya zama ubangida, wanda an kashe ‘yan adawa, sannan an tilasta wa kowa ciki har da alkalai su shiga jam’iyyarsa.

  • Obasanjo Ya Yi Tir Da Hukunce-hukuncen Zaben Gwamnoni

Tsohon shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo ya caccaki hukuncin da alkalan Nijeriya suka yanke kan shari’o’in zaben gwamnoni. Ya ce bai kamata alkalai uku zuwa biyar su soke hukuncin da miliyoyin masu kada kuri’a suka yanke a lokacin zabe ba.

Obasanjo ya bayyana ikon da wasu alkalai kalilan ke da shi a matsayin al’amari da ba za a amince da shi ba.

Tsohon shugaban kasar ya yi magana ne dangane da hukuncin da kotun daukaka kara ke ci gaba da yi kan takaddamar bayan zaden 2023 a Nijeriya.

A makon da ya gabata ne dai wasu alkalan kotun daukaka kara suka yanke hukuncin korar wasu gwamnoni uku daga kujerunsu.

Hukunce-hukuncen kotun daukaka karar sun janyo ka-ce-na-ce ne mai yiwuwa saboda duka gwamnonin jihohin da aka soke zabensu, na ‘yan adawa ne kamar babbar jam’iyyar adawa ta PDP da ke da Filato da Zamfara da kuma NNPP wadda ke da kujerar gwamnan Kano.

Lokacin da yake tsokaci a wani taron sake fasalin dimokuradiyya domin amfanin kasashen Afirka a birnin Abeokuta na Jihar Ogun, ya ce tsarin mulkin dimokuradiyya na kasashen Turawan yamma ba zai taba yin daidai da kasashen Afirka ba, kasancewar ba ya la’akari da ra’ayin mafi rinjayen al’umma.

  • Ka Iya Bakinka, Kar Ka Zubar Da Kimar Shari’a – Gwamnati

Fadar shugaban kasa ta mayar da zazzafan martani kan kalaman tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, inda ya zargi alkalai kan hukuncin da suka yanke, da kuma zargin gwamnatin Shugaba Tinubu ke haddasa lamarin.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga ya fitar, ya gargadi tsohon mataimakin shugaban kasar kan zargin gwamnati mai ci tana markushe ‘yan adawa ta hanyar amfani da bangaren shari’a.

Ya ce ya kamata Atiku ya iya bakinsa, kar ya zubar da kimar bangaren shari’a da kuma alkalai kan cimma burinsa na siyasa.

Onanuga ya ce Shugaba Tinubu masoyin dimokuradiyya ne wanda bai tsoma baki cikin hukunce-hukuncen shari’a. Ya kara da cewa PDP ta yi nasara a shari’ar kotuna a jihohin Osun da Bauchi, inda aka tabbatar da nasarar gwamna Ademola Adeleke da Bala Mohammed.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Janye ‘Yansandan Da Ke Aikin Kare Masu Hannu Da Shuni

Next Post

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

11 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

13 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

17 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

20 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.