ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Angulu

A daidai lokacin da kotun daukaka kara ke ci gaba da zartar da hukunci game da shari’o’in zabe da aka daukaka daga kotunan sauraron kararrakin zabe, hukuncin ya haifar da cacar baki a tsakanin ‘yan adawa da gwamnati, wanda wasu suka fara zargin ana yi wa dimokuradiyyar Nijeriya kafar angulu.

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayyana cewa dimokuradiyyar Nijeriya na fuskantar barazana karkashin gwamnatin APC, wanda a yanzu a bangaren shari’ar Nijeriya na sayar da hukunci kudi-a-hannu.

  • Zargin Baɗala: Hisba Ta Kama Mata Da Maza A Zamfara
  • Zaben Kano: Abba Ya Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli

Atiku ya jaddada damuwarsa kan dorewar dimokuradiyyar Nijeriya da ke fuskantar barazana na yadda jam’iyya mai mulki ke amfani da kotuna waje tsege gwamnonin ‘yan jam’iyyar adawa a jihohin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe ya fitar, ya ce ana raunata ‘yan adawa a Nijeriya ta hanyar yin magudin zabe da kuma amfani da kotuna ana amshe kujerunsu.

Ya kara da cewa, “Abin da ya fi daukar hankali shi ne, jihohin da kotuna suka yanke hukuncin cire gwamnonin dukkansu na jam’iyyun adawa ne. Tun daga Kano, Zamfara zuwa Filato, inda muke ganin cewa jam’iyya mai mulki ta kasa yin nasara a wadannan jihohi a lokacin zabe, amma kuma yanzu tana amsa a kotu.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Wadannan alamu ne masu barazana ga harkokin zabe da bangaren shari’a tare da tabbatar da cewa dimokuradiyyarmu ta lalace. A bayyana yake jam’iyya mai mulki tana gudanar da mummunar akida ta kwace mulki daga hannun ‘yan adawa.

“Abin da ya fi daukar hankali shi ne, abin da ke faruwa a yanzu a game da zaben gwamnan Filato, wanda tun farko dan majalisar APC a wani faifan bidiyo ya yi barazanar cewa jam’iyya mai mulki za ta bi tsarin shari’a don tabbatar da nasararta a kotuna.

“Saboda haka, yana nufin cewa zamanin da muke ciki a zahiri abin tsoro ne, kuma akwai jan aiki a gabanmu wajen ceto dimokuradiyyarmu daga hannun wadannan masu neman mulki ko ta wani hali.”

Sai dai Atiku ya ce ya yi mamakin abin da ke faruwa a yanzu, inda ya ce a Jihar Legas inda Shugaba kas, Bola Tinubu ya fito ya zama ubangida, wanda an kashe ‘yan adawa, sannan an tilasta wa kowa ciki har da alkalai su shiga jam’iyyarsa.

  • Obasanjo Ya Yi Tir Da Hukunce-hukuncen Zaben Gwamnoni

Tsohon shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo ya caccaki hukuncin da alkalan Nijeriya suka yanke kan shari’o’in zaben gwamnoni. Ya ce bai kamata alkalai uku zuwa biyar su soke hukuncin da miliyoyin masu kada kuri’a suka yanke a lokacin zabe ba.

Obasanjo ya bayyana ikon da wasu alkalai kalilan ke da shi a matsayin al’amari da ba za a amince da shi ba.

Tsohon shugaban kasar ya yi magana ne dangane da hukuncin da kotun daukaka kara ke ci gaba da yi kan takaddamar bayan zaden 2023 a Nijeriya.

A makon da ya gabata ne dai wasu alkalan kotun daukaka kara suka yanke hukuncin korar wasu gwamnoni uku daga kujerunsu.

Hukunce-hukuncen kotun daukaka karar sun janyo ka-ce-na-ce ne mai yiwuwa saboda duka gwamnonin jihohin da aka soke zabensu, na ‘yan adawa ne kamar babbar jam’iyyar adawa ta PDP da ke da Filato da Zamfara da kuma NNPP wadda ke da kujerar gwamnan Kano.

Lokacin da yake tsokaci a wani taron sake fasalin dimokuradiyya domin amfanin kasashen Afirka a birnin Abeokuta na Jihar Ogun, ya ce tsarin mulkin dimokuradiyya na kasashen Turawan yamma ba zai taba yin daidai da kasashen Afirka ba, kasancewar ba ya la’akari da ra’ayin mafi rinjayen al’umma.

  • Ka Iya Bakinka, Kar Ka Zubar Da Kimar Shari’a – Gwamnati

Fadar shugaban kasa ta mayar da zazzafan martani kan kalaman tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, inda ya zargi alkalai kan hukuncin da suka yanke, da kuma zargin gwamnatin Shugaba Tinubu ke haddasa lamarin.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga ya fitar, ya gargadi tsohon mataimakin shugaban kasar kan zargin gwamnati mai ci tana markushe ‘yan adawa ta hanyar amfani da bangaren shari’a.

Ya ce ya kamata Atiku ya iya bakinsa, kar ya zubar da kimar bangaren shari’a da kuma alkalai kan cimma burinsa na siyasa.

Onanuga ya ce Shugaba Tinubu masoyin dimokuradiyya ne wanda bai tsoma baki cikin hukunce-hukuncen shari’a. Ya kara da cewa PDP ta yi nasara a shari’ar kotuna a jihohin Osun da Bauchi, inda aka tabbatar da nasarar gwamna Ademola Adeleke da Bala Mohammed.

Angulu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.