• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cikin manyan batutuwa da sakatariyar baitil-malin Amurka Janet Yellen ta tabo, yayin ziyarar kwana kwanan nan da ta yi a kasar Sin, akwai zargin Sin da “Wuce Misali” a fannin bunkasa masana’antu masu alaka da makamashi mai tsafta, ciki har da na samar da ababen hawa masu aiki da lantarki.

Kafin ziyarar Yellen, kafafen watsa labaran Amurka sun yi ta yayata batun nan na “Wuce Misali” a fannin kere keren kasar Sin, suna zargin Sin din da cika kasuwannin duniya da kayayyakin fitarwa ketare masu rahusa, irin su farantan samar da lantarki ta hasken rana da ababen hawa masu aiki da lantarki.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Neman Ra’ayi Kan Aikin Tattalin Arziki

To sai dai kuma, wadannan zarge-zarge ba su da tushe ko makama. Suna kuma fayyacewa duniya halayyar masu tsara manufofi na Amurka, dake da tunanin ko kasar su ta samu, ko kuma kowa ya rasa.

Karkashin irin wannan tunani ne mahukuntan Amurka suka kakaba takunkumin hana fitar da sassan laturori na kamfanonin kasar zuwa kasuwannin Sin, da hana wasu kamfanonin Sin din damar kasuwanci na halak ta fakewa da tsaron kasa.

Har ila yau, irin wadannan matakai na nuni ga matsayin Amurka na aiwatar da manufofi idan kawai za su yi daidai da moriyar kasar, da saba musu idan za su amfani sauran sassa. Wato dai a duk lokacin da masana’antun Amurka za su ci wata gajiya, kasar na yin “Uwa da makarbiya” wajen ganin sun cimma nasara, amma idan kamfanonin kasar za su yi takara da na sauran sassan duniya, sai Amurkan ta sanya shinge na baiwa kamfanoninta kariya, wanda hakan sam ya sabawa adalci.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

A gani na, maimakon zargin “Wuce Misali” kan kamfanoni masu alaka da makamashi mai tsafta na Sin, kamata ya yi ma Amurka da sauran kasashen duniya su goyi bayan ci gaban wannan fasahohi, duba da cewa a yanzu haka ana kan wata gaba da kasashen duniya ke ta kokarin sauya alkibla zuwa amfani da nau’o’in makamashi marasa gurbatawa da dumama yanayi.

A daya bangaren kuma, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da bangarori da dama na hadin gwiwa da cin moriyar juna. Don haka ne ma har kullum, mahukuntan kasar Sin ke ganin abun da ya fi dacewa shi ne sassan biyu su ingiza ci gaban juna maimakon takawa juna birki, a dukkanin bangarori na ci gaba da aka saba da su na cinikayya, da noma, da ma sabbin fannoni irin su na kare yanayi, da fasahohi, da ayyukan kirkirarriyar basira ko AI.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Mallakar Zuciyar Maigida A Saukake

Next Post

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Related

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

3 hours ago
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar
Daga Birnin Sin

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

4 hours ago
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

4 hours ago
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

6 hours ago
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

6 hours ago
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

9 hours ago
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.