• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cikin manyan batutuwa da sakatariyar baitil-malin Amurka Janet Yellen ta tabo, yayin ziyarar kwana kwanan nan da ta yi a kasar Sin, akwai zargin Sin da “Wuce Misali” a fannin bunkasa masana’antu masu alaka da makamashi mai tsafta, ciki har da na samar da ababen hawa masu aiki da lantarki.

Kafin ziyarar Yellen, kafafen watsa labaran Amurka sun yi ta yayata batun nan na “Wuce Misali” a fannin kere keren kasar Sin, suna zargin Sin din da cika kasuwannin duniya da kayayyakin fitarwa ketare masu rahusa, irin su farantan samar da lantarki ta hasken rana da ababen hawa masu aiki da lantarki.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Neman Ra’ayi Kan Aikin Tattalin Arziki

To sai dai kuma, wadannan zarge-zarge ba su da tushe ko makama. Suna kuma fayyacewa duniya halayyar masu tsara manufofi na Amurka, dake da tunanin ko kasar su ta samu, ko kuma kowa ya rasa.

Karkashin irin wannan tunani ne mahukuntan Amurka suka kakaba takunkumin hana fitar da sassan laturori na kamfanonin kasar zuwa kasuwannin Sin, da hana wasu kamfanonin Sin din damar kasuwanci na halak ta fakewa da tsaron kasa.

Har ila yau, irin wadannan matakai na nuni ga matsayin Amurka na aiwatar da manufofi idan kawai za su yi daidai da moriyar kasar, da saba musu idan za su amfani sauran sassa. Wato dai a duk lokacin da masana’antun Amurka za su ci wata gajiya, kasar na yin “Uwa da makarbiya” wajen ganin sun cimma nasara, amma idan kamfanonin kasar za su yi takara da na sauran sassan duniya, sai Amurkan ta sanya shinge na baiwa kamfanoninta kariya, wanda hakan sam ya sabawa adalci.

Labarai Masu Nasaba

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

A gani na, maimakon zargin “Wuce Misali” kan kamfanoni masu alaka da makamashi mai tsafta na Sin, kamata ya yi ma Amurka da sauran kasashen duniya su goyi bayan ci gaban wannan fasahohi, duba da cewa a yanzu haka ana kan wata gaba da kasashen duniya ke ta kokarin sauya alkibla zuwa amfani da nau’o’in makamashi marasa gurbatawa da dumama yanayi.

A daya bangaren kuma, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da bangarori da dama na hadin gwiwa da cin moriyar juna. Don haka ne ma har kullum, mahukuntan kasar Sin ke ganin abun da ya fi dacewa shi ne sassan biyu su ingiza ci gaban juna maimakon takawa juna birki, a dukkanin bangarori na ci gaba da aka saba da su na cinikayya, da noma, da ma sabbin fannoni irin su na kare yanayi, da fasahohi, da ayyukan kirkirarriyar basira ko AI.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Mallakar Zuciyar Maigida A Saukake

Next Post

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Related

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

46 minutes ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

10 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

12 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

13 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

14 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

15 hours ago
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.